• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayin Matasa Kan Kungiyar ‘Yan Ta’adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
in Taskira
0
Ra’ayin Matasa Kan Kungiyar ‘Yan Ta’adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shafin Taskira, shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma. Tsokacimmu na yau zai yi duba ne akan wannan sabuwar kungiyar da ta fito mai suna Lakurawa. Meye ra’ayinku akan wannan sabuwar kungiya?

 

Hassan Tijjani

Sojin Nijeriya sun ce Lakurawa na da alaka da kungiyar IS kuma suna aiki a jihohin Kebbi da Skkwato, kuma sun fito ne daga kasashen Mali da jamhuriyar Nijar inda suka kutsa Nijeriya. Lokaci na farko da Lakurawa suka bayyana a Nijeriya shi ne a shekarar 2018, a lokacin da suka fara taimakawa jama’a wurin yakar ‘yan bindiga kamar yadda rahotanni suka tabbatar. To sai dai daga bisani alaka ta yi tsami tsakanin Lakurawa da mutanen gari, bayan da jama’a suka zarge su da fara sace musu shanu da kuma kakaba musu dokoki.

 

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu

Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?

Bilkisu Maharazu

Assalamu alaikum, Ra’ayina akan wannan sabuwar kungiya mai suna lakurawa ba abinda zance sai Allah ya kawo mana sauki ya kawo karshen wadannan fitintinun, domin wata majiya suna cewa wadannan kungiyoyi suma wani sa shene na Boko Haram , duk dai magana dayace da ‘yan” kidnapping domin basuda bambanci da su tunda duk ta’addanci suke ganin cewa gwamnati bata dauki wani mataki na masu garkuwa da mutaneba shi yasa suka bullo da wata kungiyar domin masu magana na cewa kowa ya samu dama sai yayi shanya domin da basu samu da maba da Basu shigo ba.

Bugu da kari, idan har ba dama suka samu ba me yasa basu shiga kuduba sai Arewa saboda anaso a bata Arewa shi yasa, Kuma a ka,ida ai ba,a shi ga kowace kasa kai tsaye batare da izini ba sai Najeriya da batada tsaro duk wanda yado za,abar shi ya shiga harda criminals saboda da zarar an bada kudi sai abude kofa a shiga batare da binciken su wayeba.

 

Usman Sani

Bayyanar wata sabuwar kungiyar ta’addanci mai suna Lakurawa a Kebbi abin damuwa ne, yana nuna bukatar karin tsaro da tattara bayanan sirri a Najeriya. Hakan kuma yana jaddada muhimmancin hadin kai tsakanin al’umma da jami’an tsaro domin gano irin wadannan barazanar da wuri da kuma magance su. Gwamnati da hukumomin tsaro suna bukatar su dauki mataki cikin gaggawa cikin hanzari kan wannan kungiya domin hana yaduwar tashin hankali da rashin kwanciyar hankali a yankin Arewacin Najeriya tunda duk masifun da futintinun daganan suke fitowa.

Muna kira da gwamnatin data dubi kirman Allah ta dubi talakawanta da sanin cewa Allah ita zai tambaya akan haka domin ta kasa kare talakawa ta dubi wannan al’amari da ayi gaggawar magance su kafin su yadu.

 

Hajiya Rukayya

Assalamu Alaikum,

Ya aiki ya kokari Allah ya taimakeku amin, nidai gaskiya Ra,ayina agameda wannan sabuwar Kungiyar ‘yan ta,adda data fito ajahar kebbi maisuna Lakurawa shine gaskiya gazawar Gwamnatice, gwamnati kiji Tsoron Allah, kutuna sai da kukayi rantsuwa da Alkar’ani akan zasu kare hakkin jama’a da dukiyoyinsu, to ya kamata kuyi kokari ku daure ansan abin akwai wahala talaka suna karkashinku kuma kune gatanmu a duba wannan lamarin da adakatar dasu tun kafin suyi karfi su gagari mutane kunsan Hausawa suna cewa ice tun yana danye ake tankwarashi idan ya ruka bazai tankwaru ba saidai ya karye. Allah ya kawo mana mafita nagode.

 

Habiba Tijjani

Assalamu alaikum!

Nidai duk da dai bansan kunkiyarba, ra’ayina akan wannan kungiyar ‘yan ta’adda da tafito a Kebbi mai suna Lakurawa to a gaskiya ni bana goyon bayan wannan kungiyar domin duk abin da za’ace ta’addanci ne to abu ne wanda yake da muni ga rayuwarmu mu mutane tunda abu ne wanda za’azo ayi ta fadace fadace da kashe kashe a rayuwa, za’azo ana ta asarar rayuka ko kuma mutane su zama cikin wahala da tashin    musamman ma talakawa domin su sukafi shan wahala a irin wannan hali idan ya taso a gaskiya ni bana goyon bayan wannan kunkiyar, muna rokon gwamnatin da ta taimaka ta tallafa cikin gaggawa tun kafi kungiyar ta yi karfi a samu a rushe wannan kungiyar idan wani abu suke nema a neme su a sasanta da a rushe wannan kungiyar idan wani abu suke bukata domin a kawo karshen wannan kungiya to a taimaka a musu. Allah ya sa mudace.

 

Fatima Abdullahi

Assalamu alaikum

Ni dai a gaskiya ra’ayina akan wannan sabuwar kungiyar mai suna Lakurawa a gaskiya duk wani mutum musulmi mai hankali wanda yake a nan kasarmu ta Nijeriya duba da yanayi da halin da muke ciki bamu kama da Boko Haram ba sannan ga garkuwa da mutane duk ba’a gama da su ba sannan a ce ga wata kuma ta fito ban da kuncin rayuwa da fama da mutane suke ciki sannan kuma a ce ga wata kunkiya ta sake fitowa gaskiya wannan al’amari abin dubawa ne. Babu wani mutum Musulmi a Nijeriya da zai goyi bayan wannan kungiyar.

Ni a ra’ayina gaskiya ba na goyon bayan wannan kungiyar domin duk abin da za’a ce zai jefa Musulmi cikin wahala da tashin hankali ai ba abin so bane, kuma daga karshe kome kan talaka zai kare. Don Allah muna kira ga gwamnatin da babbar murya da ta duba wannan lamari ta yi kokarin kawo mana karshen wadannan ‘yan ta’adda tun kafin abin ya yi karfi in sha Allahu babu abinda zai gagari gwamnati indai an sa hannu.

Mu kuma talakawa mu taya gwamnatin da jami’an tsaro da addu’a Allah ya kawo mana karshe wadannan kungiyar Allah ya nakasasu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Takaddamar Rarara Da Hukumar Tace Fina-finai Ta Jihar Kano: A Ina Gizo Ke Sakar?

Next Post

Liverpool Ta Samu Tazarar Maki 8 Akan Teburin Gasar Firimiyar Ingila

Related

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu
Taskira

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu

1 week ago
Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?
Taskira

Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?

4 weeks ago
Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
Taskira

Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma

1 month ago
Mece Ce Makomar ‘Ramadan Basket’ A Wannan Lokaci Na Matsin Tattalin Arziki?
Taskira

Mece Ce Makomar ‘Ramadan Basket’ A Wannan Lokaci Na Matsin Tattalin Arziki?

2 months ago
Me Ya Sa Wasu Yaran Ba Sa Jin Maganar Iyayensu?
Taskira

Me Ya Sa Wasu Yaran Ba Sa Jin Maganar Iyayensu?

4 months ago
Me Ke Sa Mata Gallaza Wa Yaran Da Aka Bar Musu Amana?
Taskira

Me Ke Sa Mata Gallaza Wa Yaran Da Aka Bar Musu Amana?

4 months ago
Next Post
Liverpool Ta Samu Tazarar Maki 8 Akan Teburin Gasar Firimiyar Ingila

Liverpool Ta Samu Tazarar Maki 8 Akan Teburin Gasar Firimiyar Ingila

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.