ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayin Matasa Kan Kungiyar ‘Yan Ta’adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Lakurawa

Shafin Taskira, shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma. Tsokacimmu na yau zai yi duba ne akan wannan sabuwar kungiyar da ta fito mai suna Lakurawa. Meye ra’ayinku akan wannan sabuwar kungiya?

 

Hassan Tijjani

ADVERTISEMENT

Sojin Nijeriya sun ce Lakurawa na da alaka da kungiyar IS kuma suna aiki a jihohin Kebbi da Skkwato, kuma sun fito ne daga kasashen Mali da jamhuriyar Nijar inda suka kutsa Nijeriya. Lokaci na farko da Lakurawa suka bayyana a Nijeriya shi ne a shekarar 2018, a lokacin da suka fara taimakawa jama’a wurin yakar ‘yan bindiga kamar yadda rahotanni suka tabbatar. To sai dai daga bisani alaka ta yi tsami tsakanin Lakurawa da mutanen gari, bayan da jama’a suka zarge su da fara sace musu shanu da kuma kakaba musu dokoki.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki

Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa

Bilkisu Maharazu

Assalamu alaikum, Ra’ayina akan wannan sabuwar kungiya mai suna lakurawa ba abinda zance sai Allah ya kawo mana sauki ya kawo karshen wadannan fitintinun, domin wata majiya suna cewa wadannan kungiyoyi suma wani sa shene na Boko Haram , duk dai magana dayace da ‘yan” kidnapping domin basuda bambanci da su tunda duk ta’addanci suke ganin cewa gwamnati bata dauki wani mataki na masu garkuwa da mutaneba shi yasa suka bullo da wata kungiyar domin masu magana na cewa kowa ya samu dama sai yayi shanya domin da basu samu da maba da Basu shigo ba.

Bugu da kari, idan har ba dama suka samu ba me yasa basu shiga kuduba sai Arewa saboda anaso a bata Arewa shi yasa, Kuma a ka,ida ai ba,a shi ga kowace kasa kai tsaye batare da izini ba sai Najeriya da batada tsaro duk wanda yado za,abar shi ya shiga harda criminals saboda da zarar an bada kudi sai abude kofa a shiga batare da binciken su wayeba.

 

Usman Sani

Bayyanar wata sabuwar kungiyar ta’addanci mai suna Lakurawa a Kebbi abin damuwa ne, yana nuna bukatar karin tsaro da tattara bayanan sirri a Najeriya. Hakan kuma yana jaddada muhimmancin hadin kai tsakanin al’umma da jami’an tsaro domin gano irin wadannan barazanar da wuri da kuma magance su. Gwamnati da hukumomin tsaro suna bukatar su dauki mataki cikin gaggawa cikin hanzari kan wannan kungiya domin hana yaduwar tashin hankali da rashin kwanciyar hankali a yankin Arewacin Najeriya tunda duk masifun da futintinun daganan suke fitowa.

Muna kira da gwamnatin data dubi kirman Allah ta dubi talakawanta da sanin cewa Allah ita zai tambaya akan haka domin ta kasa kare talakawa ta dubi wannan al’amari da ayi gaggawar magance su kafin su yadu.

 

Hajiya Rukayya

Assalamu Alaikum,

Ya aiki ya kokari Allah ya taimakeku amin, nidai gaskiya Ra,ayina agameda wannan sabuwar Kungiyar ‘yan ta,adda data fito ajahar kebbi maisuna Lakurawa shine gaskiya gazawar Gwamnatice, gwamnati kiji Tsoron Allah, kutuna sai da kukayi rantsuwa da Alkar’ani akan zasu kare hakkin jama’a da dukiyoyinsu, to ya kamata kuyi kokari ku daure ansan abin akwai wahala talaka suna karkashinku kuma kune gatanmu a duba wannan lamarin da adakatar dasu tun kafin suyi karfi su gagari mutane kunsan Hausawa suna cewa ice tun yana danye ake tankwarashi idan ya ruka bazai tankwaru ba saidai ya karye. Allah ya kawo mana mafita nagode.

 

Habiba Tijjani

Assalamu alaikum!

Nidai duk da dai bansan kunkiyarba, ra’ayina akan wannan kungiyar ‘yan ta’adda da tafito a Kebbi mai suna Lakurawa to a gaskiya ni bana goyon bayan wannan kungiyar domin duk abin da za’ace ta’addanci ne to abu ne wanda yake da muni ga rayuwarmu mu mutane tunda abu ne wanda za’azo ayi ta fadace fadace da kashe kashe a rayuwa, za’azo ana ta asarar rayuka ko kuma mutane su zama cikin wahala da tashin    musamman ma talakawa domin su sukafi shan wahala a irin wannan hali idan ya taso a gaskiya ni bana goyon bayan wannan kunkiyar, muna rokon gwamnatin da ta taimaka ta tallafa cikin gaggawa tun kafi kungiyar ta yi karfi a samu a rushe wannan kungiyar idan wani abu suke nema a neme su a sasanta da a rushe wannan kungiyar idan wani abu suke bukata domin a kawo karshen wannan kungiya to a taimaka a musu. Allah ya sa mudace.

 

Fatima Abdullahi

Assalamu alaikum

Ni dai a gaskiya ra’ayina akan wannan sabuwar kungiyar mai suna Lakurawa a gaskiya duk wani mutum musulmi mai hankali wanda yake a nan kasarmu ta Nijeriya duba da yanayi da halin da muke ciki bamu kama da Boko Haram ba sannan ga garkuwa da mutane duk ba’a gama da su ba sannan a ce ga wata kuma ta fito ban da kuncin rayuwa da fama da mutane suke ciki sannan kuma a ce ga wata kunkiya ta sake fitowa gaskiya wannan al’amari abin dubawa ne. Babu wani mutum Musulmi a Nijeriya da zai goyi bayan wannan kungiyar.

Ni a ra’ayina gaskiya ba na goyon bayan wannan kungiyar domin duk abin da za’a ce zai jefa Musulmi cikin wahala da tashin hankali ai ba abin so bane, kuma daga karshe kome kan talaka zai kare. Don Allah muna kira ga gwamnatin da babbar murya da ta duba wannan lamari ta yi kokarin kawo mana karshen wadannan ‘yan ta’adda tun kafin abin ya yi karfi in sha Allahu babu abinda zai gagari gwamnati indai an sa hannu.

Mu kuma talakawa mu taya gwamnatin da jami’an tsaro da addu’a Allah ya kawo mana karshe wadannan kungiyar Allah ya nakasasu.

Lakurawa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki
Taskira

Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki

May 29, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Taskira

Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa

May 24, 2026
Lakurawa
Taskira

Aure Ba Sana’a:Imani Ko Ganganci?

May 16, 2026
Next Post
Liverpool Ta Samu Tazarar Maki 8 Akan Teburin Gasar Firimiyar Ingila

Liverpool Ta Samu Tazarar Maki 8 Akan Teburin Gasar Firimiyar Ingila

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.