• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyin Kasashen Duniya Game Da Harin Da Iran Ta Kaddamar A Kan Isra’ila 

by Sadiq
1 year ago
in Kasashen Ketare, Manyan Labarai
0
Ra’ayoyin Kasashen Duniya Game Da Harin Da Iran Ta Kaddamar A Kan Isra’ila 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duniya ta kira taron gaggawa domin nazari a kan hare-haren da Iran ta kai wa Isra’ila na ramuwar gayya, yayin da kasashen duniya ke bayyana damuwa dangane da barazanar barkewar yaki a tsakanin kasashen biyu.

Sakatare Janar na majalisar, Antonio Guterres, ya yi Allah-wadai da harin, inda ya bayyana damuwa dangane da barazanar tabarbarewar al’amura a yankin gabas ta tsakiya.

  • ‘Yansanda Sun Kama Tirelar Sata Da Kayan Miliyan 30 A Bauchi
  • ‘Yan Ta’adda Sun Yi Yunƙurin Ƙwace Iko Da Sakatariyar Jihar Oyo

Shugabar gudanarwar kungiyar kasashen Turai, Ursula von der Leyen ta bukaci Iran da ta gaggauta tsagaita wuta da kuma kiran kasashen da su tsagaita wuta tare da aiki tare domin tabbatar da zaman lafiya.

Sakatare Janar na kungiyar kawancen tsaro ta NATO, Jens Stoltenberg ya ce sun yi Allah-wadai da abin da ya kira matakin na Iran, yayin da suke ci gaba da sanya ido a kan abin da ke faruwa.

Firaministan Birtaniya, Rishi Sunak, ya bayyana harin na Iran a matsayin na rashin hankali, wanda ke iya fadada tashin hankalin da ke gudana a gabas ta tsakiya.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

Firaministan Canada Justin Trudeau ya soki harin na Iran, inda ya sake jaddada goyan bayan kasarsa ga Isra’ila.

Ita kuwa China ta bayyana harin na Iran a matsayin fadadar rikicin Gaza, inda ta bukaci aiwatar da kudirin kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya domin tabbatar da tsagaita wuta da kuma kawo karshen rikicin.

China ta bukaci kasashen duniya musamman masu karfin fada a ji domin ganin sun taka rawar ganin wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin baki daya.

Kasar Masar ta bayyana matukar damuwa da tashin hankalin tare da bukatar taka-tsan-tsan domin kaucewa fadawa yaki.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi Allah-wadai da harin Iran a kan Isra’ila, wanda ya bayyana shi a matsayin abin da ka iya jefa daukacin yankin cikin tashin hankali.

Shugaban gwamnatin Jamus, Olaf Scholz ya bayyana harin na Iran a matsayin rashin hankali.

Ita kuwa Rasha ta bayyana damuwa da harin, tare da samun taka-tsan-tsan, kamar yadda Qatar ta bukaci manyan kasashen duniya daukar matakin kwantar da hankalin bangarorin.

Kasar Saudi Arabiya ta yi kira ga bangarorin biyu da su kai zuciya nesa domin kare yankin gabas ta tsakiya.

Shugaban Amurka, Joe Biden, ya bayyana goyon bayansa ga Isra’ila bayan ganawa da manyan jami’an tsaron kasar, yayin da ya ce za su ci gaba da tallafa wa kasar.

Sauran kasashen da suka bayyana matsayi dangane da harin sun hada da Ukraine da Turkiya da Italiya da kuma Spain.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hare-HareIranIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Bayyana Damuwa Game Da Halin Da Ake Ciki Tsakanin Iran Da Isra’ila

Next Post

Zan Daga Darajar Wasanni A Kebbi – Gwamna Nasir Idris

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

54 minutes ago
Ministan Tsaro
Manyan Labarai

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

1 hour ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

10 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanaki 10 A Faransa Da Birtaniya

15 hours ago
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki
Manyan Labarai

Gargaɗi: Ƙauyuka 43 A Jihohi 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa 

17 hours ago
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

20 hours ago
Next Post
Zan Daga Darajar Wasanni A Kebbi – Gwamna Nasir Idris

Zan Daga Darajar Wasanni A Kebbi - Gwamna Nasir Idris

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Dakatar Da Karuwar Hare-hare A Kan Likitoci – Ra’ayinmu

Barazanar Yajin Aiki: Likitoci Sun Bai Wa Gwamnati Wa’adin Kwana 10

September 5, 2025
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Ministan Tsaro

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

September 5, 2025
Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.