• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyin PDP, PRP Da SDP Kan Gudanar Da Zabe A Kano

by Mustapha Ibrahim
3 years ago
Kano

Wasu daga cikin ‘yan takara a jam’iyyar PDP, SDP, PRP a Kano sun bayyana ra’ayoyinsu kan yadda hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) karkashin shugabancin Ambasada Abdullahi Zango, ta gabatar da zaben ta a Kano.

Shugaban matasa na jam’iyyar PDP, Hon Salisu Dani ya ce yadda Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tsara na hana ba da kudi domin a zabi mutum ya yi daidai. Ya ce hakan ne zai sa a samu dimokuradiyya mai tsafta a Nijeriya.

  • Kotu Ta Yanke Wa Murja Hukuncin Sharar Asibiti A Kano

Dan takarar majalisa a PDP, Hon Rabiu Sale Wangal ya ce wannan ya ba su kwarin giwar yin nasara a zaban.

Shi kuwa, tsohun ma’aji a jam’iyyar APC kuma dan takarar gwamnan Kano a jam’iyyar SDP, Hon Bala Muhammad Gwagwarwa ya ce duk abin da za a yi a tsaya kan gaskiya kuma a bi a hankali domin babu wani abu da zai tafi daidai ba tare da kwatatanta gaskiya ba, kuma akwai bukatar tsarin da zai amfani al’umar kasa a matakan kananan hukumomi ta hanyar ba su kudadansu daga gwamnatin tarayya kai-tsaye yadda za a iya rage matsaloli da talauci.

A nasa bangaren, shugaban jam’iyyar PRP na Kano, Injiniya Abba Namatazo ya ce zaban da hukumar INEC ta gabatar a kasa baki daya su dai sun gamsu da yadda hukumar ta gabatar da zabe, amma rashin nasarar PRP ta samu ne sakamakon goguwan sauyi a siyasance.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Ya ce a baya an yi guguwar PRP, inda aka zabi jam’iyyar a Kano a shekarar 1979, sannan kuma an samu guguwar jam’iyyar APC a 2015 da 2019, kuma wata rana za a dawo a sake yin PRP.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe Mutum 1, Sun Ceto 14 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

Sojoji Sun Kashe Mutum 1, Sun Ceto 14 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.