• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Ko Atiku Abubakar Da PDP Ta Tsayar Zai Iya Kai Bantensa A Zaben 2023?

by Aisha Seyoji
3 years ago
in Siyasa
0
Ra’ayoyinku A Kan Ko Atiku Abubakar Da PDP Ta Tsayar Zai Iya Kai Bantensa A Zaben 2023?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Barkanmu da sake saduwa a filinmu na Ra’ayi Riga,Wannan mako za musgabatar muku da ra’ayoyinku ne a kan tsayar da Atiku Abubakar da aka yi a matsayin dan takarar shugabancin Nijeriya a jam’iyyar PDP a karshen makon jiya, shin a ganinku zai iya kai bantensa kuwa.

Man Nass
Wannan shi ne abin da muka fi kyautata masa zato musamman a wannan lokaci da mutane suke cikin matsanancin rayuwa wanda gani ake yi kamar jam’iyya mai mulki bata yi wa al’umma abinda zai rage musu radadi ba.

  • INEC Ta Fitar Da Sabbin Ka’idojin Zaben 2023

Bashir Ibrahim Matazu
Idan an yi aiki tukuru zai iya kai labari idan kuma ‘yan PDP suka maida hankali ak an zagin wasu da suke hamayya za su iya komawa gidan jiya. Allah Ya ba mai rabo sa a.

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta
Allah wadaran na ka ya lalace… A wannan filin mai albarka mun tattauna magana a kan zaben fidda gwani, inda mu ka ce Delegets su yi gaskiya amma sai gashi labara ya zo cewa, Atiku ya kashe su da iyayen kudade sun zabe shi.
Don haka Atiku zai iya kaiwa ga ci, tun da lamarin na kudi ne, Allah ya ba mu shuwagabanni na gari.

Omar Naseer Imam
Muna fatan Atiku ya zama alkhairi a gare mu duk da bamu da zabi fatanmu Allah ya bamu wanda zai zama mafita ga al’umman Nijeriya gaba daya, arewaci da kuma kudancinta Alfarman Annabi Muhammad (SAW)

Labarai Masu Nasaba

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Sani Bello Kano
Wallahu galibun ala amrihi, to babban abin dubawa anan shi ne yadda yake sakarwa deligets kudi kamar hauka, sannan kuma indai a haka za a tafi to lallae zai iya samun mulki tunda sai abinda suka ce sannan kuri’ar talaka bata da amfani sai abinda INEC suka ce, sannan kuma suma ba zai barsu haka ba, sai dai addu’ar Allah ya zaba mana mafi alkhairi.

Cmrd Sadeek Rufa’i Ɗanguguwa
Allah wadaran Zaben fidda gwani irin wannan. Duk da irin kiraye kiraye da gidan Jaridu da malamai suka yi ta yi wurin tsarkaka niyya ga dukkan masu alhakin fidda dan takara, amman sai da suka kauce ta hanyar amsar kudade. Allah ya kyauta wannan lamari.

Nuruddeen Muhammad Funtua
A gaskiya mutane sun sha wahala a wannan mulkin na APC duba da yanayin kuncin rayuwa da ake ciki to idan akai duba da hakan zai iya kaiwa ga nasara. Amma mu yawancin ‘yan Nijeria mun tura lamarin ga Allah ne domin zabin Allah shi ne zabi. Mudai Allah ya zaba mana shugabanni nagari, idan shi ne alkairi Allah ya bamu ikon zabarsa.

Ibrahim Hassan Baban Adila
Anawa tunanin inaga Atiku Abubakar zai iya kai labari duba da duk ‘yantakarar da suka fito basu da karfin da za su kara dashi, sannan kuma yadda analysis yanuna yawancin yan arewa za su yi Atiku kuma yankin arewa sun fi kudu yawa sosai, sannan mutane sun gaji da jam’iyyar APC sakamakon gazawar da ta yi wajen mulki, abubuwa sun tabarbare ba kamar yadda suka zo suka sami kasar ba. Daga karshe mu talakawa muna rokon Allah ya zaba mana shugaba nagari kuma mafi alkhairi a gare mu Amen, daga Ibrahim Hassan Minister Baban Adila da ansar Jihar Gombe.

Muhd Basheer Sa’ad
Duba da yadda al’amura suka tabarbare wa Shugaba Buhari tabbas APC za ta sha kayi ne.
Shi kuwa Atiku shima ba wani labari da zai kai duk da cewar yana da magoya baya.
Allah dai ya zaba mana shugaba mafi alhairi ga rayuwar mu, amin

Sani Ladan
To lallai wannan batu na takarar Atiku babbar nasara ce ga yankin mu na arewa kuma gaskiya wannan karon Atikun zai iya kai bantensa a kakar zabe mai zuwa duba da yadda ita jam’iyya mai mulki ta Gaza sauke nauyin da yake kanta,muna fatan Allah ya zaba mana mafi allhairi

Saimas Spices
Gamu nan dai kuma a game na siyasar Nijeriya, bamu da ikon jayyaya da deligete wanda idan ba an canza tsarin zaben deligates din bama siyasa ba za ta gyaru ba, mu dai talakan Nijeriya zamu ci gaba da addu’ar Allah ya zaba mana mafi alkhairi

Maman Aisha
To ai wannan abin sai Allah kawai, sai dai fatan mu Allah ya bamu nagari wanda zai yi abinda ya dace damu ‘yan Nijeriya, Allah ya ba mu sa a

Moubarak Abdoullahee
Aslm mudae ayanzu bazamu iya fadan cewa ze iya kai bantennasaba ko Aa, harsemunga yadda ta kaya azaben fidda gwani na jam iyar APC domin ance darashin uwa ake uwar daki

Nura Usman Idris
Da wahala gaskiya duba da yadda Talakawa suka yi masa bakin fenti.

It’z Sam Dambatta
To ita dai siyasa mace ce da ciki amma gaskiya abin da kamar wuya, musamman idan a kace jagoran kwankwasiya ya tsaya a jam’iyar NNPP. Mu dai fatan mu Allah ya zaba mana mafi alkhairi

Khadija Muhammad
Zabin Allah shi ne zabi, Allah ya zaba mana mafi alhairi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tikitin Tsayawa Takarar Aisha Binani Ya Karfafa Siyasar Matan Arewa

Next Post

2023: Ta Tabbata Kauran Bauchi Ne Dan Takarar PDP A Gwamnan Bauchi

Related

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu
Siyasa

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

21 hours ago
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP
Siyasa

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

2 days ago
Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

4 days ago
Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi
Siyasa

Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi

1 week ago
Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani
Siyasa

Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani

1 week ago
Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba
Labarai

Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba

1 week ago
Next Post
2023: Ta Tabbata Kauran Bauchi Ne Dan Takarar PDP A Gwamnan Bauchi

2023: Ta Tabbata Kauran Bauchi Ne Dan Takarar PDP A Gwamnan Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

May 12, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

May 12, 2025
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

May 12, 2025
A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.