• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Ruwan Sama Marka-marka Da Ake Yi A Sassan Nijeriya

by Aisha Seyoji
3 years ago
Ruwan sama

A yau mun kawo muku ra’ayoyin masu karatun mune a kan halin da ake ciki a yankunan su bayan ruwan sama kamar da bakin kwarya da ake fuskanta a wasu jihohin Arewacin Nijeriya a ‘yan kwanakin nan.

Ibrahim Hassan Baban Adila
Gaskiya bana kam a garin Gombe mun samu ambaliyar ruwan sama musamman a yankin kananan hukumomin Jihar Gombe irin su Bajoga da Kwami da sauransu sai dai matsalar gwamnati ta yi ko inkula da su gaskiya, daga karshe muna kira da gwamnoni dasu dubi lamarin don kawo gyara tara da bayar da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa.

Sakodaga ibrahim Hassan Minister Abban Adila da Ansar jihar Gombe.

It’z Sam Dambatta
To mu dai anan yankinmu Alhmdulillah domin cikin ikon Allah da rushewar gidaje ko ambaliyar ruwa duk da sauki a wannan yankin namu. Muna kara gode wa Allah da wannan ni’ima

Umar Ibrahim Umar
Alhamdulillah gaskiya dai damunar bana ba’a cewa komai sai dai addu’a Allah ya bamu wucewa lafiya wanda ta yi sanadiyar rasuwarsu Allah ya karbi shahadarsu wanda suka yi asarar dukiya kuma Allah ya mayar musu da alheri, Amin

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

It’z Jameel Moh’d
Masha Allah, a nan jihar Taraba mu dai alhmdullah sai dai mu yi adu’ar fatan zaman lafiya mu girbe abinda muka shuga lafiya cikin kwanciyar hankali

Adamu Yunusa Ibrahim
Inda mu ke kam babu wata matsala. Alhamdulillah

Rah’iss Abba Lawan
Mu kam Alhamdulillahi bamu da matsala da ruwan sama

Abdulmumini Sese
Har mun fara girbi

Isma’il Hussain Musa
Mu kam sai godiya, Allah ya kara mana lafiya

Nuruddeen Muhammad Funtua
Ina fatan alkhairi a gareku baki daya yan uwa da abokan arziki. Mudai a namu yanki sai dai godiya ga Allah madaukakin Sarki, ruwa kam ba a cewa komai, muna adu’ar Allah ya sa muga karshen ruwan lafiya, ya bamu damina mai albarka

Sani Ladan
Mudai kam a namu yanki sai godiya domin amfanin gonakinmu na kara kyau, muna fatan girbi mai kyau sakamakon wadataccen ruwan sama amma duk da haka ba a rasa asarar gine-gine ba Allah ya bamu alkhairan da ke cikin wannan damina

Engr Abdullahi Musbahu Dambatta
Fatan mu shi ne ubangiji ya bamu mai albarka wanda kuma za mu iya sarrafawa

Yusuf Muhammad Jalingo
Mu a namu yankin (Gombe) sai godiya saboda wasu wuraren kamar su Bajoga da ke karamar hukumar Funakaye an samu asarar rayuka da dukiyar al’umma. Haka a jiya ma an sami yankewar wani hanya a wassu wuraren sai dai a kwaryar jiha abin da sauki kadan. Muna jan hankulan ‘yan uwa ake kulawa da magudanan ruwa saboda gujewa ambaliya, Allah ya bamu damuna mai albarka. Amiin

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta
A gaskiya mu a Katsina Alhamdu-lillah, ana samun ruwa sosai sosai. Sannan kuma dai akwai saukin ambaliyar ruwa, kuma gidaje ba su cika rushewa kamar shekarun baya. Allah ka ba mu damina mai albarka ya kawo mana zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Shamsi Umar Bakanike Dambatta
Tabbas a wannan mako and akko maudu’i mai matukar muhimmachi duba da yadda aka sha ruwa kamar da bakin kwarya, toh muma dai anan karamar hukumar Dambatta haka abin yake kamar yadda aka sha mamakon wannan ruwa a wurare daban-daban sai dai mu anan karamar hukumar Dambatta an sami rugujewar gine-gine domin kuwa a wasu yankin ma na karamar hukumar Dambatta hadda asarar rai da aka samu dama asarar dukiya da fatan dai Allah yajikan wanda suka rasu ya kuma kiyaye faruwar hakan anan gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Next Post
Ambaliyar Ruwa: Mutum 4 Sun Mutu, 8,400 Sun Bar Gidajensu A Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Mutum 4 Sun Mutu, 8,400 Sun Bar Gidajensu A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.