• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Shirin Buhari Na Kara Wa Ma’aikata Alawus

by yahuzajere
3 years ago
in Rahotonni
0
Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya ne Ministan Kwadago Dakta Chris Ingige ya sanar da cewa, gwamantin tarayya ta fara shirye-shiryen ganin an kara wa ma’aikatan gwamnatin tarayya alawus don ya yi daidai da yadda ake samun hauhawar farashinn kayyakin masarufi. Shin hakan zai rage radadin matsalar tattalin arziki da hauhawar farashin kayan masarufi da ake fama da shi? Ga dai yadda masu bibiyarmu suka bayyana nasu ra’ayinsu.

Mohammed Inuwa
Zai taimaka matuka in aka lura da yadda ma’aikatan ke cikin wani hali saboda tsadar kayayyakin masarufi da kuma tsadar rayuwa da ake ciki. Kuma yakamata gwamnati ta kawo hukumar kula da daidaiton farashin kayan masarufi, kuma ta bude wasu wajajen sayar wa talakawa kayan masarufi mai sauki domin taimakonsu. Nagode.

Nuruddeen Muhammad Funtua
A gaskiya na ji dadin haka saboda tsadar kayan yau da gobe, insha Allah zai rage radadin hakan alfarmar Shugaba (s.a.w.)

Sani Ladan
A a ba zai rage radadi da matsalar hauhawar kaya ba sai dai ma ya karu domin idan kace gwamnatin tarayya ta yi wa ma’aikatanta karin albashi kuma bata kayyade farashin kaya ba lallai ‘yan kasuwa sun sami hanyar yi wa kayansu karin kudi yadda suka ga dama, amma abinda yafi dacewa gwamnati ta yi shi ne kayyade farashin kayan masarufi wannan ita ce hanyar farko ta nemawa ma’aikata saukin rayuwa amma ba karin albashi ba koda za ta yi karin to ya zama ta kula da farashin kaya, muna rokon Allah ya kawo mana sauki a rayuwar mu.

Kabo Idris Saminu
A gaskiya wannan ba zai rage ba domin ai an yi a baya kuma ba a ga wani canji ba abin da gwamnati ya dace ta yi shi ne ta daidai ta farashi shi ne kawai ba wai karin albashi ba da a kasar babu tsayayen farashi kullum sai hauhawa yake yi.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Real Miftahu Ahmad Panda
A’a, ba na tsammanin yin karin albashi ga ma’aikata, zai kawo karshen halin matsin tattalin arziki, ko hauhawar farashin da mu ke tsaka da fama da ita, a kasar nan, duba da cewar, a duk lokacin da aka yi batun za a kara wa Ma’aikata albashi, muna ganin yadda farashin kayayyaki su ke ninninkawa, tun ma kafin a yi karin, hakan ya kansa ko da bayan an yi, sai a rasa a ina alfanun da ake tsammanin samu ya makale.
Ni a ganina, daukar matakan da za su daga darajar takardar kudi ta Naira, shi yafi muhimmanci, a kan yin karin Albashin, duba da yadda tattalin arzikin mu ya dogara da Dalar Amurka, ina ganin idan aka farfado da darajar Naira, to tabbas komai zai yi sauki.

Abdul’aziz Mohammed
Muna muku barka da warhaka. A gskiya ata wanii fannin hakan abin a yaba ne zai iya kawo saukin rayuwa kadan amma ga ma’aikatan gwamnatin tarayya, saboda idan muka duba karin da aka yi a baya na naira dubu 30 har yandu wasu jihohi da dama sun kasa aiwatar dashi.

Abin yi babba ga gwamnatin tarayya shi ne ta yi kokarin kawo tsare tsare da tabbatar dasu wanda zai tabbatar da rage hau_hau kayan masarufi. Allah ya taimaki kasar mu Nijeriya ameen.

Comr Hassan S Umar
Toh gaskiya dai abin lura a nan shi ne a duk lokacin da aka samu karin albashi idan ka tsaya zaka ji tashin kayan masarufi ya biyo baya, karshe karin da za a samu sai ya wuce abin da gwamnati takara a albashin ma’aikata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tsaurara Tsaro Gabanin Ziyarar Buhari A Adamawa

Next Post

DA DUMI-DUMI: ‘Yansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Filato

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

7 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

2 weeks ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

3 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 weeks ago
Next Post
DA DUMI-DUMI: ‘Yansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Filato

DA DUMI-DUMI: 'Yansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.