• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Shirin Buhari Na Kara Wa Ma’aikata Alawus

by yahuzajere
2 years ago
in Rahotonni
0
Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya ne Ministan Kwadago Dakta Chris Ingige ya sanar da cewa, gwamantin tarayya ta fara shirye-shiryen ganin an kara wa ma’aikatan gwamnatin tarayya alawus don ya yi daidai da yadda ake samun hauhawar farashinn kayyakin masarufi. Shin hakan zai rage radadin matsalar tattalin arziki da hauhawar farashin kayan masarufi da ake fama da shi? Ga dai yadda masu bibiyarmu suka bayyana nasu ra’ayinsu.

Mohammed Inuwa
Zai taimaka matuka in aka lura da yadda ma’aikatan ke cikin wani hali saboda tsadar kayayyakin masarufi da kuma tsadar rayuwa da ake ciki. Kuma yakamata gwamnati ta kawo hukumar kula da daidaiton farashin kayan masarufi, kuma ta bude wasu wajajen sayar wa talakawa kayan masarufi mai sauki domin taimakonsu. Nagode.

Nuruddeen Muhammad Funtua
A gaskiya na ji dadin haka saboda tsadar kayan yau da gobe, insha Allah zai rage radadin hakan alfarmar Shugaba (s.a.w.)

Sani Ladan
A a ba zai rage radadi da matsalar hauhawar kaya ba sai dai ma ya karu domin idan kace gwamnatin tarayya ta yi wa ma’aikatanta karin albashi kuma bata kayyade farashin kaya ba lallai ‘yan kasuwa sun sami hanyar yi wa kayansu karin kudi yadda suka ga dama, amma abinda yafi dacewa gwamnati ta yi shi ne kayyade farashin kayan masarufi wannan ita ce hanyar farko ta nemawa ma’aikata saukin rayuwa amma ba karin albashi ba koda za ta yi karin to ya zama ta kula da farashin kaya, muna rokon Allah ya kawo mana sauki a rayuwar mu.

Kabo Idris Saminu
A gaskiya wannan ba zai rage ba domin ai an yi a baya kuma ba a ga wani canji ba abin da gwamnati ya dace ta yi shi ne ta daidai ta farashi shi ne kawai ba wai karin albashi ba da a kasar babu tsayayen farashi kullum sai hauhawa yake yi.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Real Miftahu Ahmad Panda
A’a, ba na tsammanin yin karin albashi ga ma’aikata, zai kawo karshen halin matsin tattalin arziki, ko hauhawar farashin da mu ke tsaka da fama da ita, a kasar nan, duba da cewar, a duk lokacin da aka yi batun za a kara wa Ma’aikata albashi, muna ganin yadda farashin kayayyaki su ke ninninkawa, tun ma kafin a yi karin, hakan ya kansa ko da bayan an yi, sai a rasa a ina alfanun da ake tsammanin samu ya makale.
Ni a ganina, daukar matakan da za su daga darajar takardar kudi ta Naira, shi yafi muhimmanci, a kan yin karin Albashin, duba da yadda tattalin arzikin mu ya dogara da Dalar Amurka, ina ganin idan aka farfado da darajar Naira, to tabbas komai zai yi sauki.

Abdul’aziz Mohammed
Muna muku barka da warhaka. A gskiya ata wanii fannin hakan abin a yaba ne zai iya kawo saukin rayuwa kadan amma ga ma’aikatan gwamnatin tarayya, saboda idan muka duba karin da aka yi a baya na naira dubu 30 har yandu wasu jihohi da dama sun kasa aiwatar dashi.

Abin yi babba ga gwamnatin tarayya shi ne ta yi kokarin kawo tsare tsare da tabbatar dasu wanda zai tabbatar da rage hau_hau kayan masarufi. Allah ya taimaki kasar mu Nijeriya ameen.

Comr Hassan S Umar
Toh gaskiya dai abin lura a nan shi ne a duk lokacin da aka samu karin albashi idan ka tsaya zaka ji tashin kayan masarufi ya biyo baya, karshe karin da za a samu sai ya wuce abin da gwamnati takara a albashin ma’aikata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tsaurara Tsaro Gabanin Ziyarar Buhari A Adamawa

Next Post

DA DUMI-DUMI: ‘Yansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Filato

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Buhari
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
DA DUMI-DUMI: ‘Yansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Filato

DA DUMI-DUMI: 'Yansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.