ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Shirin Buhari Na Kara Wa Ma’aikata Alawus

by yahuzajere
4 years ago
Buhari

Kwanakin baya ne Ministan Kwadago Dakta Chris Ingige ya sanar da cewa, gwamantin tarayya ta fara shirye-shiryen ganin an kara wa ma’aikatan gwamnatin tarayya alawus don ya yi daidai da yadda ake samun hauhawar farashinn kayyakin masarufi. Shin hakan zai rage radadin matsalar tattalin arziki da hauhawar farashin kayan masarufi da ake fama da shi? Ga dai yadda masu bibiyarmu suka bayyana nasu ra’ayinsu.

Mohammed Inuwa
Zai taimaka matuka in aka lura da yadda ma’aikatan ke cikin wani hali saboda tsadar kayayyakin masarufi da kuma tsadar rayuwa da ake ciki. Kuma yakamata gwamnati ta kawo hukumar kula da daidaiton farashin kayan masarufi, kuma ta bude wasu wajajen sayar wa talakawa kayan masarufi mai sauki domin taimakonsu. Nagode.

Nuruddeen Muhammad Funtua
A gaskiya na ji dadin haka saboda tsadar kayan yau da gobe, insha Allah zai rage radadin hakan alfarmar Shugaba (s.a.w.)

ADVERTISEMENT

Sani Ladan
A a ba zai rage radadi da matsalar hauhawar kaya ba sai dai ma ya karu domin idan kace gwamnatin tarayya ta yi wa ma’aikatanta karin albashi kuma bata kayyade farashin kaya ba lallai ‘yan kasuwa sun sami hanyar yi wa kayansu karin kudi yadda suka ga dama, amma abinda yafi dacewa gwamnati ta yi shi ne kayyade farashin kayan masarufi wannan ita ce hanyar farko ta nemawa ma’aikata saukin rayuwa amma ba karin albashi ba koda za ta yi karin to ya zama ta kula da farashin kaya, muna rokon Allah ya kawo mana sauki a rayuwar mu.

Kabo Idris Saminu
A gaskiya wannan ba zai rage ba domin ai an yi a baya kuma ba a ga wani canji ba abin da gwamnati ya dace ta yi shi ne ta daidai ta farashi shi ne kawai ba wai karin albashi ba da a kasar babu tsayayen farashi kullum sai hauhawa yake yi.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Real Miftahu Ahmad Panda
A’a, ba na tsammanin yin karin albashi ga ma’aikata, zai kawo karshen halin matsin tattalin arziki, ko hauhawar farashin da mu ke tsaka da fama da ita, a kasar nan, duba da cewar, a duk lokacin da aka yi batun za a kara wa Ma’aikata albashi, muna ganin yadda farashin kayayyaki su ke ninninkawa, tun ma kafin a yi karin, hakan ya kansa ko da bayan an yi, sai a rasa a ina alfanun da ake tsammanin samu ya makale.
Ni a ganina, daukar matakan da za su daga darajar takardar kudi ta Naira, shi yafi muhimmanci, a kan yin karin Albashin, duba da yadda tattalin arzikin mu ya dogara da Dalar Amurka, ina ganin idan aka farfado da darajar Naira, to tabbas komai zai yi sauki.

Abdul’aziz Mohammed
Muna muku barka da warhaka. A gskiya ata wanii fannin hakan abin a yaba ne zai iya kawo saukin rayuwa kadan amma ga ma’aikatan gwamnatin tarayya, saboda idan muka duba karin da aka yi a baya na naira dubu 30 har yandu wasu jihohi da dama sun kasa aiwatar dashi.

Abin yi babba ga gwamnatin tarayya shi ne ta yi kokarin kawo tsare tsare da tabbatar dasu wanda zai tabbatar da rage hau_hau kayan masarufi. Allah ya taimaki kasar mu Nijeriya ameen.

Comr Hassan S Umar
Toh gaskiya dai abin lura a nan shi ne a duk lokacin da aka samu karin albashi idan ka tsaya zaka ji tashin kayan masarufi ya biyo baya, karshe karin da za a samu sai ya wuce abin da gwamnati takara a albashin ma’aikata.

Buhari
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
DA DUMI-DUMI: ‘Yansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Filato

DA DUMI-DUMI: 'Yansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.