ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Shirin Buhari Na Kara Wa Ma’aikata Alawus

by yahuzajere
3 years ago
Buhari

Kwanakin baya ne Ministan Kwadago Dakta Chris Ingige ya sanar da cewa, gwamantin tarayya ta fara shirye-shiryen ganin an kara wa ma’aikatan gwamnatin tarayya alawus don ya yi daidai da yadda ake samun hauhawar farashinn kayyakin masarufi. Shin hakan zai rage radadin matsalar tattalin arziki da hauhawar farashin kayan masarufi da ake fama da shi? Ga dai yadda masu bibiyarmu suka bayyana nasu ra’ayinsu.

Mohammed Inuwa
Zai taimaka matuka in aka lura da yadda ma’aikatan ke cikin wani hali saboda tsadar kayayyakin masarufi da kuma tsadar rayuwa da ake ciki. Kuma yakamata gwamnati ta kawo hukumar kula da daidaiton farashin kayan masarufi, kuma ta bude wasu wajajen sayar wa talakawa kayan masarufi mai sauki domin taimakonsu. Nagode.

Nuruddeen Muhammad Funtua
A gaskiya na ji dadin haka saboda tsadar kayan yau da gobe, insha Allah zai rage radadin hakan alfarmar Shugaba (s.a.w.)

ADVERTISEMENT

Sani Ladan
A a ba zai rage radadi da matsalar hauhawar kaya ba sai dai ma ya karu domin idan kace gwamnatin tarayya ta yi wa ma’aikatanta karin albashi kuma bata kayyade farashin kaya ba lallai ‘yan kasuwa sun sami hanyar yi wa kayansu karin kudi yadda suka ga dama, amma abinda yafi dacewa gwamnati ta yi shi ne kayyade farashin kayan masarufi wannan ita ce hanyar farko ta nemawa ma’aikata saukin rayuwa amma ba karin albashi ba koda za ta yi karin to ya zama ta kula da farashin kaya, muna rokon Allah ya kawo mana sauki a rayuwar mu.

Kabo Idris Saminu
A gaskiya wannan ba zai rage ba domin ai an yi a baya kuma ba a ga wani canji ba abin da gwamnati ya dace ta yi shi ne ta daidai ta farashi shi ne kawai ba wai karin albashi ba da a kasar babu tsayayen farashi kullum sai hauhawa yake yi.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Real Miftahu Ahmad Panda
A’a, ba na tsammanin yin karin albashi ga ma’aikata, zai kawo karshen halin matsin tattalin arziki, ko hauhawar farashin da mu ke tsaka da fama da ita, a kasar nan, duba da cewar, a duk lokacin da aka yi batun za a kara wa Ma’aikata albashi, muna ganin yadda farashin kayayyaki su ke ninninkawa, tun ma kafin a yi karin, hakan ya kansa ko da bayan an yi, sai a rasa a ina alfanun da ake tsammanin samu ya makale.
Ni a ganina, daukar matakan da za su daga darajar takardar kudi ta Naira, shi yafi muhimmanci, a kan yin karin Albashin, duba da yadda tattalin arzikin mu ya dogara da Dalar Amurka, ina ganin idan aka farfado da darajar Naira, to tabbas komai zai yi sauki.

Abdul’aziz Mohammed
Muna muku barka da warhaka. A gskiya ata wanii fannin hakan abin a yaba ne zai iya kawo saukin rayuwa kadan amma ga ma’aikatan gwamnatin tarayya, saboda idan muka duba karin da aka yi a baya na naira dubu 30 har yandu wasu jihohi da dama sun kasa aiwatar dashi.

Abin yi babba ga gwamnatin tarayya shi ne ta yi kokarin kawo tsare tsare da tabbatar dasu wanda zai tabbatar da rage hau_hau kayan masarufi. Allah ya taimaki kasar mu Nijeriya ameen.

Comr Hassan S Umar
Toh gaskiya dai abin lura a nan shi ne a duk lokacin da aka samu karin albashi idan ka tsaya zaka ji tashin kayan masarufi ya biyo baya, karshe karin da za a samu sai ya wuce abin da gwamnati takara a albashin ma’aikata.

Buhari
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Buhari
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Buhari
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
DA DUMI-DUMI: ‘Yansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Filato

DA DUMI-DUMI: 'Yansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.