• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya

by Abubakar Abba and Sulaiman
12 months ago
in Noma Da Kiwo
0
IFAD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa rahoton da aka samu na tattalin arzikin kasa, ya nuna habakar noma a Nijeriya ta ragu da kashi 1.4 cikin 100; sakamakon tabarbarewar rashin tsaro da tsadar kayan noma a wannan fanni na aikin noma a cikin zango na biyu na shekarar 2024.

 

A cikin shekara guda, fannin ya karu da kashi 1. 41 cikin 100 daga kashi 1.50 a cikin 100, wanda kuma fannin ya sake samun raguwa da kashi 0.09 a cikin 100 a shekarar 2023.

  • Me Ya Sa Masu Noman Albasa Ke Samun Karamar Riba A Nijeriya?
  • Zamfara: Yadda Zargin Juna Da Hannu A Ta’addanci Ya Yi Kamari Tsakanin Dauda Da Matawalle

Haka zalik, daga zango zuwa zango; fannin ya samu karuwa da kashi 0.18 cikin 100.

 

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Babban jami’i a cibiyar kasuwanci mai zaman kanta, Muda Yusuf; a wata hira da ya yi da Jaridar BusinessDay, ya bayyana cewa; kalubalen rashin tsaro a kasar, shi ne babban matsalar da ke shafar fannin, wanda hakan ya tilasta wa manoma yin watsi da gonakinsu; inda hakan kuma ya kara haifar da hauhawar farashin kayan abinci a fadin kasar.

 

Muda ya yi nuni da cewa, sai a magance kalubalen rashin tsaro a wannan kasa; kafin a iya magance kalubalen hauhawar farashin kayan abinci.

 

Shi kuwa, wani kwararre a fannin aikin noma da bai bukaci a bayyana sunansa ba ya sanar da cewa, fannin na matukar fusknatar koma baya.

 

Har ila yau, wani rahoton hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ya nuna cewa, fannin na taimaka wa tattalin arizkin kasar da kusan  kashi 22.61 cikin 100.

 

Sai dai, a fannin cikin zango na biyu na 2023, ya taimaka da kashi 23.01 cikin 100; wanda ya dara na zango na daya a 2024, da ya kai matsayin kashi 21.07 cikin 100.

 

Kola Aderibigbe, shugaban dangogin fannin aikin noma; kuma shugaban kungiyar kasuwanci da masana’antu, reshen Jihar Legas a wata hira da aka yi da shi a kwanakin baya ya ce, “A yanzu, manoma na daukar hayar jami’an tsro masu zaman kansu ne, domin kare gonakinsu da amfanin da suka shuka da kuma kawunansu”.

 

Haka zalika, wani rahoton sirri na (SBM); wanda yake mayar da hankali kan kasuwar Afrika da kuma fannin tsaro ya bayyana cewa, daga 2020 zuwa 2024; sama da manoma 1,356 ‘yan bindiga suka hallaka a Arewacin Nijeriya, wanda hakan kuma ya jawo gaza yin noma tare da haifar da hauhawar farashin kayan abinci da kuma dakatar da masu son zuba jari a fannin.

 

Shi ma babban jami’i a kamfanin tuntuba na akin noma Florunsho Olayemi Sammorf ya sanar da cewa, “Duk hekta guda ta noma yanzu ta rubunya, wanda ya ce; hakan ya sanya manoma rage yawan hektar da suke nomawa kari kuma da kalubalen rashin tsaro, inda hakan ya kara jawo hauhawar farashin kayan abinci”.

 

Fannin aikin noma na wannan kasa, shi ne kan gaba wajen samar da kashi 87.48 cikin 100, wanda ake samun akalla Naira  tiriliyan 9.8 a zango na biyu na 2024.

 

Bugu da kari, a kwanakin baya; hukumar samar da abinci da harkar aikin noma ta duniya (FAO) ta sanar da cewa, ‘yan Nijeriya sama da miliyan 31.8; na fuskantar karancin abinci, wanda hakan ya jawo rashin samun abinci mai gina jiki, musamman a tsakanin mata da yara a daukacin fadin wannan kasa.

 

Har ila yau, a cikin wani rahoton na kungiyar ‘Cadre Harmonise’ da ke sa ido a kan samar da wadataccen abinci da ta fitar bisa hadaka da hukumar kasuwanci ta kasa da kasa ta ‘GIZ’ da ke da shalkwata a Kasar Jamus sun nuna cewa, an samu hauhawar farashin kayan abinci, sakamakon cire tallafin iskar gas da kuma fuskantar kalubalen rashin tsaro, wanda hakan ya jefa ‘yan Nijeriya cikin halin kuncin rayuwa.

 

Har ila yau, Nijeriya na fuskantar mummunar hauhawar farashin kayan abinci da ya kai kashi 40 cikin 100 a wannan shekara ta 2024 tare da koma baya a bangaren noma da kuma fuskanta tsadar kayan aikin noma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Rashin TsaroTa'addanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

Next Post

An Bude Taron Birni Mai Ayyukan Tsara Abubuwa Na Kasa Da Kasa Na 2024 A Shanghai

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

6 days ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

6 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
An Bude Taron Birni Mai Ayyukan Tsara Abubuwa Na Kasa Da Kasa Na 2024 A Shanghai

An Bude Taron Birni Mai Ayyukan Tsara Abubuwa Na Kasa Da Kasa Na 2024 A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.