ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
IFAD

Bisa rahoton da aka samu na tattalin arzikin kasa, ya nuna habakar noma a Nijeriya ta ragu da kashi 1.4 cikin 100; sakamakon tabarbarewar rashin tsaro da tsadar kayan noma a wannan fanni na aikin noma a cikin zango na biyu na shekarar 2024.

 

A cikin shekara guda, fannin ya karu da kashi 1. 41 cikin 100 daga kashi 1.50 a cikin 100, wanda kuma fannin ya sake samun raguwa da kashi 0.09 a cikin 100 a shekarar 2023.

ADVERTISEMENT
  • Me Ya Sa Masu Noman Albasa Ke Samun Karamar Riba A Nijeriya?
  • Zamfara: Yadda Zargin Juna Da Hannu A Ta’addanci Ya Yi Kamari Tsakanin Dauda Da Matawalle

Haka zalik, daga zango zuwa zango; fannin ya samu karuwa da kashi 0.18 cikin 100.

 

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Babban jami’i a cibiyar kasuwanci mai zaman kanta, Muda Yusuf; a wata hira da ya yi da Jaridar BusinessDay, ya bayyana cewa; kalubalen rashin tsaro a kasar, shi ne babban matsalar da ke shafar fannin, wanda hakan ya tilasta wa manoma yin watsi da gonakinsu; inda hakan kuma ya kara haifar da hauhawar farashin kayan abinci a fadin kasar.

 

Muda ya yi nuni da cewa, sai a magance kalubalen rashin tsaro a wannan kasa; kafin a iya magance kalubalen hauhawar farashin kayan abinci.

 

Shi kuwa, wani kwararre a fannin aikin noma da bai bukaci a bayyana sunansa ba ya sanar da cewa, fannin na matukar fusknatar koma baya.

 

Har ila yau, wani rahoton hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ya nuna cewa, fannin na taimaka wa tattalin arizkin kasar da kusan  kashi 22.61 cikin 100.

 

Sai dai, a fannin cikin zango na biyu na 2023, ya taimaka da kashi 23.01 cikin 100; wanda ya dara na zango na daya a 2024, da ya kai matsayin kashi 21.07 cikin 100.

 

Kola Aderibigbe, shugaban dangogin fannin aikin noma; kuma shugaban kungiyar kasuwanci da masana’antu, reshen Jihar Legas a wata hira da aka yi da shi a kwanakin baya ya ce, “A yanzu, manoma na daukar hayar jami’an tsro masu zaman kansu ne, domin kare gonakinsu da amfanin da suka shuka da kuma kawunansu”.

 

Haka zalika, wani rahoton sirri na (SBM); wanda yake mayar da hankali kan kasuwar Afrika da kuma fannin tsaro ya bayyana cewa, daga 2020 zuwa 2024; sama da manoma 1,356 ‘yan bindiga suka hallaka a Arewacin Nijeriya, wanda hakan kuma ya jawo gaza yin noma tare da haifar da hauhawar farashin kayan abinci da kuma dakatar da masu son zuba jari a fannin.

 

Shi ma babban jami’i a kamfanin tuntuba na akin noma Florunsho Olayemi Sammorf ya sanar da cewa, “Duk hekta guda ta noma yanzu ta rubunya, wanda ya ce; hakan ya sanya manoma rage yawan hektar da suke nomawa kari kuma da kalubalen rashin tsaro, inda hakan ya kara jawo hauhawar farashin kayan abinci”.

 

Fannin aikin noma na wannan kasa, shi ne kan gaba wajen samar da kashi 87.48 cikin 100, wanda ake samun akalla Naira  tiriliyan 9.8 a zango na biyu na 2024.

 

Bugu da kari, a kwanakin baya; hukumar samar da abinci da harkar aikin noma ta duniya (FAO) ta sanar da cewa, ‘yan Nijeriya sama da miliyan 31.8; na fuskantar karancin abinci, wanda hakan ya jawo rashin samun abinci mai gina jiki, musamman a tsakanin mata da yara a daukacin fadin wannan kasa.

 

Har ila yau, a cikin wani rahoton na kungiyar ‘Cadre Harmonise’ da ke sa ido a kan samar da wadataccen abinci da ta fitar bisa hadaka da hukumar kasuwanci ta kasa da kasa ta ‘GIZ’ da ke da shalkwata a Kasar Jamus sun nuna cewa, an samu hauhawar farashin kayan abinci, sakamakon cire tallafin iskar gas da kuma fuskantar kalubalen rashin tsaro, wanda hakan ya jefa ‘yan Nijeriya cikin halin kuncin rayuwa.

 

Har ila yau, Nijeriya na fuskantar mummunar hauhawar farashin kayan abinci da ya kai kashi 40 cikin 100 a wannan shekara ta 2024 tare da koma baya a bangaren noma da kuma fuskanta tsadar kayan aikin noma.

Noma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
Noma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
An Bude Taron Birni Mai Ayyukan Tsara Abubuwa Na Kasa Da Kasa Na 2024 A Shanghai

An Bude Taron Birni Mai Ayyukan Tsara Abubuwa Na Kasa Da Kasa Na 2024 A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.