ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
IFAD

Bisa rahoton da aka samu na tattalin arzikin kasa, ya nuna habakar noma a Nijeriya ta ragu da kashi 1.4 cikin 100; sakamakon tabarbarewar rashin tsaro da tsadar kayan noma a wannan fanni na aikin noma a cikin zango na biyu na shekarar 2024.

 

A cikin shekara guda, fannin ya karu da kashi 1. 41 cikin 100 daga kashi 1.50 a cikin 100, wanda kuma fannin ya sake samun raguwa da kashi 0.09 a cikin 100 a shekarar 2023.

ADVERTISEMENT
  • Me Ya Sa Masu Noman Albasa Ke Samun Karamar Riba A Nijeriya?
  • Zamfara: Yadda Zargin Juna Da Hannu A Ta’addanci Ya Yi Kamari Tsakanin Dauda Da Matawalle

Haka zalik, daga zango zuwa zango; fannin ya samu karuwa da kashi 0.18 cikin 100.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Babban jami’i a cibiyar kasuwanci mai zaman kanta, Muda Yusuf; a wata hira da ya yi da Jaridar BusinessDay, ya bayyana cewa; kalubalen rashin tsaro a kasar, shi ne babban matsalar da ke shafar fannin, wanda hakan ya tilasta wa manoma yin watsi da gonakinsu; inda hakan kuma ya kara haifar da hauhawar farashin kayan abinci a fadin kasar.

 

Muda ya yi nuni da cewa, sai a magance kalubalen rashin tsaro a wannan kasa; kafin a iya magance kalubalen hauhawar farashin kayan abinci.

 

Shi kuwa, wani kwararre a fannin aikin noma da bai bukaci a bayyana sunansa ba ya sanar da cewa, fannin na matukar fusknatar koma baya.

 

Har ila yau, wani rahoton hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ya nuna cewa, fannin na taimaka wa tattalin arizkin kasar da kusan  kashi 22.61 cikin 100.

 

Sai dai, a fannin cikin zango na biyu na 2023, ya taimaka da kashi 23.01 cikin 100; wanda ya dara na zango na daya a 2024, da ya kai matsayin kashi 21.07 cikin 100.

 

Kola Aderibigbe, shugaban dangogin fannin aikin noma; kuma shugaban kungiyar kasuwanci da masana’antu, reshen Jihar Legas a wata hira da aka yi da shi a kwanakin baya ya ce, “A yanzu, manoma na daukar hayar jami’an tsro masu zaman kansu ne, domin kare gonakinsu da amfanin da suka shuka da kuma kawunansu”.

 

Haka zalika, wani rahoton sirri na (SBM); wanda yake mayar da hankali kan kasuwar Afrika da kuma fannin tsaro ya bayyana cewa, daga 2020 zuwa 2024; sama da manoma 1,356 ‘yan bindiga suka hallaka a Arewacin Nijeriya, wanda hakan kuma ya jawo gaza yin noma tare da haifar da hauhawar farashin kayan abinci da kuma dakatar da masu son zuba jari a fannin.

 

Shi ma babban jami’i a kamfanin tuntuba na akin noma Florunsho Olayemi Sammorf ya sanar da cewa, “Duk hekta guda ta noma yanzu ta rubunya, wanda ya ce; hakan ya sanya manoma rage yawan hektar da suke nomawa kari kuma da kalubalen rashin tsaro, inda hakan ya kara jawo hauhawar farashin kayan abinci”.

 

Fannin aikin noma na wannan kasa, shi ne kan gaba wajen samar da kashi 87.48 cikin 100, wanda ake samun akalla Naira  tiriliyan 9.8 a zango na biyu na 2024.

 

Bugu da kari, a kwanakin baya; hukumar samar da abinci da harkar aikin noma ta duniya (FAO) ta sanar da cewa, ‘yan Nijeriya sama da miliyan 31.8; na fuskantar karancin abinci, wanda hakan ya jawo rashin samun abinci mai gina jiki, musamman a tsakanin mata da yara a daukacin fadin wannan kasa.

 

Har ila yau, a cikin wani rahoton na kungiyar ‘Cadre Harmonise’ da ke sa ido a kan samar da wadataccen abinci da ta fitar bisa hadaka da hukumar kasuwanci ta kasa da kasa ta ‘GIZ’ da ke da shalkwata a Kasar Jamus sun nuna cewa, an samu hauhawar farashin kayan abinci, sakamakon cire tallafin iskar gas da kuma fuskantar kalubalen rashin tsaro, wanda hakan ya jefa ‘yan Nijeriya cikin halin kuncin rayuwa.

 

Har ila yau, Nijeriya na fuskantar mummunar hauhawar farashin kayan abinci da ya kai kashi 40 cikin 100 a wannan shekara ta 2024 tare da koma baya a bangaren noma da kuma fuskanta tsadar kayan aikin noma.

Noma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
Noma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
An Bude Taron Birni Mai Ayyukan Tsara Abubuwa Na Kasa Da Kasa Na 2024 A Shanghai

An Bude Taron Birni Mai Ayyukan Tsara Abubuwa Na Kasa Da Kasa Na 2024 A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.