ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
IFAD

Bisa rahoton da aka samu na tattalin arzikin kasa, ya nuna habakar noma a Nijeriya ta ragu da kashi 1.4 cikin 100; sakamakon tabarbarewar rashin tsaro da tsadar kayan noma a wannan fanni na aikin noma a cikin zango na biyu na shekarar 2024.

 

A cikin shekara guda, fannin ya karu da kashi 1. 41 cikin 100 daga kashi 1.50 a cikin 100, wanda kuma fannin ya sake samun raguwa da kashi 0.09 a cikin 100 a shekarar 2023.

ADVERTISEMENT
  • Me Ya Sa Masu Noman Albasa Ke Samun Karamar Riba A Nijeriya?
  • Zamfara: Yadda Zargin Juna Da Hannu A Ta’addanci Ya Yi Kamari Tsakanin Dauda Da Matawalle

Haka zalik, daga zango zuwa zango; fannin ya samu karuwa da kashi 0.18 cikin 100.

 

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Babban jami’i a cibiyar kasuwanci mai zaman kanta, Muda Yusuf; a wata hira da ya yi da Jaridar BusinessDay, ya bayyana cewa; kalubalen rashin tsaro a kasar, shi ne babban matsalar da ke shafar fannin, wanda hakan ya tilasta wa manoma yin watsi da gonakinsu; inda hakan kuma ya kara haifar da hauhawar farashin kayan abinci a fadin kasar.

 

Muda ya yi nuni da cewa, sai a magance kalubalen rashin tsaro a wannan kasa; kafin a iya magance kalubalen hauhawar farashin kayan abinci.

 

Shi kuwa, wani kwararre a fannin aikin noma da bai bukaci a bayyana sunansa ba ya sanar da cewa, fannin na matukar fusknatar koma baya.

 

Har ila yau, wani rahoton hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ya nuna cewa, fannin na taimaka wa tattalin arizkin kasar da kusan  kashi 22.61 cikin 100.

 

Sai dai, a fannin cikin zango na biyu na 2023, ya taimaka da kashi 23.01 cikin 100; wanda ya dara na zango na daya a 2024, da ya kai matsayin kashi 21.07 cikin 100.

 

Kola Aderibigbe, shugaban dangogin fannin aikin noma; kuma shugaban kungiyar kasuwanci da masana’antu, reshen Jihar Legas a wata hira da aka yi da shi a kwanakin baya ya ce, “A yanzu, manoma na daukar hayar jami’an tsro masu zaman kansu ne, domin kare gonakinsu da amfanin da suka shuka da kuma kawunansu”.

 

Haka zalika, wani rahoton sirri na (SBM); wanda yake mayar da hankali kan kasuwar Afrika da kuma fannin tsaro ya bayyana cewa, daga 2020 zuwa 2024; sama da manoma 1,356 ‘yan bindiga suka hallaka a Arewacin Nijeriya, wanda hakan kuma ya jawo gaza yin noma tare da haifar da hauhawar farashin kayan abinci da kuma dakatar da masu son zuba jari a fannin.

 

Shi ma babban jami’i a kamfanin tuntuba na akin noma Florunsho Olayemi Sammorf ya sanar da cewa, “Duk hekta guda ta noma yanzu ta rubunya, wanda ya ce; hakan ya sanya manoma rage yawan hektar da suke nomawa kari kuma da kalubalen rashin tsaro, inda hakan ya kara jawo hauhawar farashin kayan abinci”.

 

Fannin aikin noma na wannan kasa, shi ne kan gaba wajen samar da kashi 87.48 cikin 100, wanda ake samun akalla Naira  tiriliyan 9.8 a zango na biyu na 2024.

 

Bugu da kari, a kwanakin baya; hukumar samar da abinci da harkar aikin noma ta duniya (FAO) ta sanar da cewa, ‘yan Nijeriya sama da miliyan 31.8; na fuskantar karancin abinci, wanda hakan ya jawo rashin samun abinci mai gina jiki, musamman a tsakanin mata da yara a daukacin fadin wannan kasa.

 

Har ila yau, a cikin wani rahoton na kungiyar ‘Cadre Harmonise’ da ke sa ido a kan samar da wadataccen abinci da ta fitar bisa hadaka da hukumar kasuwanci ta kasa da kasa ta ‘GIZ’ da ke da shalkwata a Kasar Jamus sun nuna cewa, an samu hauhawar farashin kayan abinci, sakamakon cire tallafin iskar gas da kuma fuskantar kalubalen rashin tsaro, wanda hakan ya jefa ‘yan Nijeriya cikin halin kuncin rayuwa.

 

Har ila yau, Nijeriya na fuskantar mummunar hauhawar farashin kayan abinci da ya kai kashi 40 cikin 100 a wannan shekara ta 2024 tare da koma baya a bangaren noma da kuma fuskanta tsadar kayan aikin noma.

Noma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Noma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
An Bude Taron Birni Mai Ayyukan Tsara Abubuwa Na Kasa Da Kasa Na 2024 A Shanghai

An Bude Taron Birni Mai Ayyukan Tsara Abubuwa Na Kasa Da Kasa Na 2024 A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.