ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Masu Noman Albasa Ke Samun Karamar Riba A Nijeriya?

by Abubakar Abba
2 years ago
Albasa

Hukumar kula da fitar kaya ta kasa (NEPC), ta nuna damuwarta kan rashin samun riba mai yawa daga hada-hadar kasuwancin Alabsar, duk kuwa da cewa; Nijeriya na daya daga cikin kasashen da ke gaba a fadin Afirka wajen nomanta.    

Duk da cewa, a duk shekara ana noman Albasa kimanin tan miliyan biyu, amma adadin Albasar da ake nomawa a kasar ya yi matukar yin kasa, wanda hakan na faruwa ne sakamakon amfani da gundarin Albasar wajen yin wasu nau’ikan abubuwa daban-daban a wannan kasa.

  • Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya
  • Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo

Hai ila yau, masu ruwa da tsaki ne suka bayyana haka; a wani taron tattauwa a kan dabarun bunkasa nomanta da aka gudanar a Jihar Gombe.

ADVERTISEMENT

Babbar Darakta ta hukumar NEPC, Nonye Ayeni a jawabinta a wajen taron, ta bayyana kalubalen da ake fuskanta a bangaren hada-hadar kasuwancin Albasar a Nijeriya.

Kazalika, ta sanar da haka ne; ta hanyar wakilinta a wajen taron Mustapha Umar Faruk, inda ya bayyana cewa; an jawo jihohi kamar su Gombe, Sakkwato, Kebbi, Zamfara, Katsina, Kano, Kaduna, Jigawa, Yobe, Borno, Bauchi, Taraba, Filato da kuma Abuja, a wannan fanni na noman Albasar.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Ta ci gaba da cewa, sai dai har yanzu Nijeriya ta gaza ci gaba da rike matsayinta a faninn hada-hadar kasuwancin na Albasa, musamman sakamakon rashin iya sarrafa ta da kuma yin amfani da dabarun fitar da ita zuwa kasashen ketare.

Nonye ta kara da cewa, saboda rashin kimanta Albsar a kasar nan ne, yasa ake samun raguwar samun ribarta da kuma raguwar saumun kudaden shiga daga fitar da ita da ake yi zuwa kasashen ketare.

A cewarta, wannan dalili ne yasa hukumar ta hanyar wannan shiri ta samu nasarar tattaunawa da masu ruwa da tsaki, domin bunkasa dabarun fitar da ita zuwa kasashen ketare.

A cewar tata, hakan zai bai wa Nijeriya damar aiwatar da gasa a kasuwannin duniya, musamman a wannan bangare na hada-hadar kasuwancin Albasa, a tsakaninta da sauran kasashen duniya.

Nasiru Aliyu, Kwamishina Ma’aikatar Kasuwanci da Zuba Jari; yaba wa hukumar ya yi a kan shirya taron. Inda ya sanar da cewa, taron ya zo a kan gaba duba da karuwar wayar da kan manoman Albasar.

Kwamishinan, wanda Babban Sakatare a Ma’aikatar; Babayo Hassan Abubakar ya wakilta a wajen taron, ya bukaci manomanta su kara yin kokari wajen noma ta; ba tare da dogaro ga gwamnati ba.

Shi kuwa, Shugaban Kungiyar Manoman Albasa na Shiyyar Arewa Maso Gabas; Alhaji Sani Pantami; yaba wa hukumar ya yi a kan ilimantar da manoman da sauran masu ruwa da tsaki da ta yi, musamman a kan muhimmancin kasuwancin Albasa na kasa da kasa.

Ya kuma yi waiwaye a kan kalubalen da manoman suke fuskanta a baya, da suka hada da yin asara sakamakon rashin kwarewar da suke da ita na fitar da Albasar zuwa kasashen na ketare, domin sayar da ita.

Sai dai, ya yi nuni da cewa; bisa ilimin da suka samu ta hanyar shirin ya ce, yana da yakinin cewa; akasarin manoman a halin yanzu zai ba su kwarin gwiwar sanin dabarun noman Albasar, musamman ta hanyar samun ingantaccen Irin nomanta.

Albasa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (6)

Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (6)

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.