ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Masu Noman Albasa Ke Samun Karamar Riba A Nijeriya?

by Abubakar Abba
2 years ago
Albasa

Hukumar kula da fitar kaya ta kasa (NEPC), ta nuna damuwarta kan rashin samun riba mai yawa daga hada-hadar kasuwancin Alabsar, duk kuwa da cewa; Nijeriya na daya daga cikin kasashen da ke gaba a fadin Afirka wajen nomanta.    

Duk da cewa, a duk shekara ana noman Albasa kimanin tan miliyan biyu, amma adadin Albasar da ake nomawa a kasar ya yi matukar yin kasa, wanda hakan na faruwa ne sakamakon amfani da gundarin Albasar wajen yin wasu nau’ikan abubuwa daban-daban a wannan kasa.

  • Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya
  • Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo

Hai ila yau, masu ruwa da tsaki ne suka bayyana haka; a wani taron tattauwa a kan dabarun bunkasa nomanta da aka gudanar a Jihar Gombe.

ADVERTISEMENT

Babbar Darakta ta hukumar NEPC, Nonye Ayeni a jawabinta a wajen taron, ta bayyana kalubalen da ake fuskanta a bangaren hada-hadar kasuwancin Albasar a Nijeriya.

Kazalika, ta sanar da haka ne; ta hanyar wakilinta a wajen taron Mustapha Umar Faruk, inda ya bayyana cewa; an jawo jihohi kamar su Gombe, Sakkwato, Kebbi, Zamfara, Katsina, Kano, Kaduna, Jigawa, Yobe, Borno, Bauchi, Taraba, Filato da kuma Abuja, a wannan fanni na noman Albasar.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Ta ci gaba da cewa, sai dai har yanzu Nijeriya ta gaza ci gaba da rike matsayinta a faninn hada-hadar kasuwancin na Albasa, musamman sakamakon rashin iya sarrafa ta da kuma yin amfani da dabarun fitar da ita zuwa kasashen ketare.

Nonye ta kara da cewa, saboda rashin kimanta Albsar a kasar nan ne, yasa ake samun raguwar samun ribarta da kuma raguwar saumun kudaden shiga daga fitar da ita da ake yi zuwa kasashen ketare.

A cewarta, wannan dalili ne yasa hukumar ta hanyar wannan shiri ta samu nasarar tattaunawa da masu ruwa da tsaki, domin bunkasa dabarun fitar da ita zuwa kasashen ketare.

A cewar tata, hakan zai bai wa Nijeriya damar aiwatar da gasa a kasuwannin duniya, musamman a wannan bangare na hada-hadar kasuwancin Albasa, a tsakaninta da sauran kasashen duniya.

Nasiru Aliyu, Kwamishina Ma’aikatar Kasuwanci da Zuba Jari; yaba wa hukumar ya yi a kan shirya taron. Inda ya sanar da cewa, taron ya zo a kan gaba duba da karuwar wayar da kan manoman Albasar.

Kwamishinan, wanda Babban Sakatare a Ma’aikatar; Babayo Hassan Abubakar ya wakilta a wajen taron, ya bukaci manomanta su kara yin kokari wajen noma ta; ba tare da dogaro ga gwamnati ba.

Shi kuwa, Shugaban Kungiyar Manoman Albasa na Shiyyar Arewa Maso Gabas; Alhaji Sani Pantami; yaba wa hukumar ya yi a kan ilimantar da manoman da sauran masu ruwa da tsaki da ta yi, musamman a kan muhimmancin kasuwancin Albasa na kasa da kasa.

Ya kuma yi waiwaye a kan kalubalen da manoman suke fuskanta a baya, da suka hada da yin asara sakamakon rashin kwarewar da suke da ita na fitar da Albasar zuwa kasashen na ketare, domin sayar da ita.

Sai dai, ya yi nuni da cewa; bisa ilimin da suka samu ta hanyar shirin ya ce, yana da yakinin cewa; akasarin manoman a halin yanzu zai ba su kwarin gwiwar sanin dabarun noman Albasar, musamman ta hanyar samun ingantaccen Irin nomanta.

Albasa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (6)

Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (6)

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.