ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Masu Noman Albasa Ke Samun Karamar Riba A Nijeriya?

by Abubakar Abba
2 years ago
Albasa

Hukumar kula da fitar kaya ta kasa (NEPC), ta nuna damuwarta kan rashin samun riba mai yawa daga hada-hadar kasuwancin Alabsar, duk kuwa da cewa; Nijeriya na daya daga cikin kasashen da ke gaba a fadin Afirka wajen nomanta.    

Duk da cewa, a duk shekara ana noman Albasa kimanin tan miliyan biyu, amma adadin Albasar da ake nomawa a kasar ya yi matukar yin kasa, wanda hakan na faruwa ne sakamakon amfani da gundarin Albasar wajen yin wasu nau’ikan abubuwa daban-daban a wannan kasa.

  • Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya
  • Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo

Hai ila yau, masu ruwa da tsaki ne suka bayyana haka; a wani taron tattauwa a kan dabarun bunkasa nomanta da aka gudanar a Jihar Gombe.

ADVERTISEMENT

Babbar Darakta ta hukumar NEPC, Nonye Ayeni a jawabinta a wajen taron, ta bayyana kalubalen da ake fuskanta a bangaren hada-hadar kasuwancin Albasar a Nijeriya.

Kazalika, ta sanar da haka ne; ta hanyar wakilinta a wajen taron Mustapha Umar Faruk, inda ya bayyana cewa; an jawo jihohi kamar su Gombe, Sakkwato, Kebbi, Zamfara, Katsina, Kano, Kaduna, Jigawa, Yobe, Borno, Bauchi, Taraba, Filato da kuma Abuja, a wannan fanni na noman Albasar.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

Ta ci gaba da cewa, sai dai har yanzu Nijeriya ta gaza ci gaba da rike matsayinta a faninn hada-hadar kasuwancin na Albasa, musamman sakamakon rashin iya sarrafa ta da kuma yin amfani da dabarun fitar da ita zuwa kasashen ketare.

Nonye ta kara da cewa, saboda rashin kimanta Albsar a kasar nan ne, yasa ake samun raguwar samun ribarta da kuma raguwar saumun kudaden shiga daga fitar da ita da ake yi zuwa kasashen ketare.

A cewarta, wannan dalili ne yasa hukumar ta hanyar wannan shiri ta samu nasarar tattaunawa da masu ruwa da tsaki, domin bunkasa dabarun fitar da ita zuwa kasashen ketare.

A cewar tata, hakan zai bai wa Nijeriya damar aiwatar da gasa a kasuwannin duniya, musamman a wannan bangare na hada-hadar kasuwancin Albasa, a tsakaninta da sauran kasashen duniya.

Nasiru Aliyu, Kwamishina Ma’aikatar Kasuwanci da Zuba Jari; yaba wa hukumar ya yi a kan shirya taron. Inda ya sanar da cewa, taron ya zo a kan gaba duba da karuwar wayar da kan manoman Albasar.

Kwamishinan, wanda Babban Sakatare a Ma’aikatar; Babayo Hassan Abubakar ya wakilta a wajen taron, ya bukaci manomanta su kara yin kokari wajen noma ta; ba tare da dogaro ga gwamnati ba.

Shi kuwa, Shugaban Kungiyar Manoman Albasa na Shiyyar Arewa Maso Gabas; Alhaji Sani Pantami; yaba wa hukumar ya yi a kan ilimantar da manoman da sauran masu ruwa da tsaki da ta yi, musamman a kan muhimmancin kasuwancin Albasa na kasa da kasa.

Ya kuma yi waiwaye a kan kalubalen da manoman suke fuskanta a baya, da suka hada da yin asara sakamakon rashin kwarewar da suke da ita na fitar da Albasar zuwa kasashen na ketare, domin sayar da ita.

Sai dai, ya yi nuni da cewa; bisa ilimin da suka samu ta hanyar shirin ya ce, yana da yakinin cewa; akasarin manoman a halin yanzu zai ba su kwarin gwiwar sanin dabarun noman Albasar, musamman ta hanyar samun ingantaccen Irin nomanta.

Albasa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (6)

Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (6)

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.