• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya kaddamar da shirin rabon kayan abinci na watan Ramadan, domin a rage radadin wahalhalu ga al’ummar jihar.

Gwamnan, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabinsa na kaddamar da rabon abincin don ci gaban manufofin jin-kai na gwamnatinsa.

  • Al’adar Tashe A Kasar Hausa
  • ÆŠaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun KarÉ“ar Abincin Tallafi

A yayin da yake bayyanawa taron jama’ar cewa” gwamntinsa ta yi hakan ne daga jama’a don taimaka wa mabukata da kuma bayar da agaji ga wadanda matsalolin zamantakewa da tattalin arziki ya shafa.

“Hanya ce ta nuna hadin kai da goyon baya ga jama’a da kuma yadda za su iya samun albarkatu don ci gaban rayuwarsu.

“Wannan alama ce ta al’umma da kuma zama majibincin É—an uwan juna.”

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

A cewar gwamnan, rabon hatsin shi ma wani mataki ne na wucin gadi na samar da tallafi ga al’ummar jihar baki daya.

Ya kuma umarci duk wadanda aka damka wa hatsin da su tabbatar an bai wa daukacin al’ummar jihar kasonsu.

Ya kara da cewa, “Gwamnatin Jihar Kebbi ita ce gwamnatin al’umma, don haka ya kamata a raba kayan abinci ba tare da nuna bambancin addini ko kabilancin ba.

“Siyasa ta kare, an gama zabe, abin da ya rage shi ne shugabanci na gari, bai kamata a bar kowa ba, babu bambancin jam’iyya.

Ya kuma gargadi kwamitocin rabon kayayyaki a dukkan matakai kan duk wani nau’i na mataki kar a siyar da su, ko kuma karkatar da hatsin da aka yi tanadi don mutanen jihar.

Ya kuma yi gargadin cewa duk wani jami’in gwamnati da aka samu yana karkatar da hatsi za a hukunta shi, wanda zai kai ga tsige shi daga mukaminsa, ya kuma umarci shugabannin hukumomin tsaro da su tabbatar da bin ka’ida gaba daya ko kuma a kama duk wanda aka samu da laifi a hukunta shi.

Tun da farko kwamishinan noma, Alhaji Shehu Mu’azu ya yaba wa gwamnan bisa amincewa da sayan buhunan iri-iri domin jin dadin jama’arsa.

Ya kuma yaba da kyawawan halayen Gwamna Nasir Idris zuwa ga jama’ar jih6ar Kebbi kan wannan tsari da ya kaddamar na rabon abinci a duk fadin jihar.

Mu’azu ya sanar wa mahalarta taron cewa abin da aka kaddamar don rabawa kashi ashirin ne na hatsin da gwamnati ta saya yayin da za a yi rabon sauran a ma’auni daga baya a matakai.

Ya ce tuni aka aike da hatsin da ke tara a dukkanin kananan hukumomin 21 zuwa hedikwatar kananan hukumomin don raba wa ga al’ummar yankunan.

Daga karshe Kwamishinan ya bayyana irin kayan abincin da gwamnatin jihar ta sayo don rabawa ga watan azumin Ramadana sun hada da Gero, dawa da kuma shinkafa da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna NasirKebbirabon kayan abinciRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’adar Tashe A Kasar Hausa

Next Post

Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Aiwatar Da Haramcin Kamun Kifi Na Tsawon Shekaru 10 A Kogin Yangtze

Related

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

1 hour ago
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa
Labarai

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

2 hours ago
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya
Labarai

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

3 hours ago
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC
Labarai

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

4 hours ago
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya
Labarai

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

7 hours ago
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa
Labarai

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

8 hours ago
Next Post
sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Aiwatar Da Haramcin Kamun Kifi Na Tsawon Shekaru 10 A Kogin Yangtze

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.