• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya kaddamar da shirin rabon kayan abinci na watan Ramadan, domin a rage radadin wahalhalu ga al’ummar jihar.

Gwamnan, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabinsa na kaddamar da rabon abincin don ci gaban manufofin jin-kai na gwamnatinsa.

  • Al’adar Tashe A Kasar Hausa
  • ÆŠaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun KarÉ“ar Abincin Tallafi

A yayin da yake bayyanawa taron jama’ar cewa” gwamntinsa ta yi hakan ne daga jama’a don taimaka wa mabukata da kuma bayar da agaji ga wadanda matsalolin zamantakewa da tattalin arziki ya shafa.

“Hanya ce ta nuna hadin kai da goyon baya ga jama’a da kuma yadda za su iya samun albarkatu don ci gaban rayuwarsu.

“Wannan alama ce ta al’umma da kuma zama majibincin É—an uwan juna.”

Labarai Masu Nasaba

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

A cewar gwamnan, rabon hatsin shi ma wani mataki ne na wucin gadi na samar da tallafi ga al’ummar jihar baki daya.

Ya kuma umarci duk wadanda aka damka wa hatsin da su tabbatar an bai wa daukacin al’ummar jihar kasonsu.

Ya kara da cewa, “Gwamnatin Jihar Kebbi ita ce gwamnatin al’umma, don haka ya kamata a raba kayan abinci ba tare da nuna bambancin addini ko kabilancin ba.

“Siyasa ta kare, an gama zabe, abin da ya rage shi ne shugabanci na gari, bai kamata a bar kowa ba, babu bambancin jam’iyya.

Ya kuma gargadi kwamitocin rabon kayayyaki a dukkan matakai kan duk wani nau’i na mataki kar a siyar da su, ko kuma karkatar da hatsin da aka yi tanadi don mutanen jihar.

Ya kuma yi gargadin cewa duk wani jami’in gwamnati da aka samu yana karkatar da hatsi za a hukunta shi, wanda zai kai ga tsige shi daga mukaminsa, ya kuma umarci shugabannin hukumomin tsaro da su tabbatar da bin ka’ida gaba daya ko kuma a kama duk wanda aka samu da laifi a hukunta shi.

Tun da farko kwamishinan noma, Alhaji Shehu Mu’azu ya yaba wa gwamnan bisa amincewa da sayan buhunan iri-iri domin jin dadin jama’arsa.

Ya kuma yaba da kyawawan halayen Gwamna Nasir Idris zuwa ga jama’ar jih6ar Kebbi kan wannan tsari da ya kaddamar na rabon abinci a duk fadin jihar.

Mu’azu ya sanar wa mahalarta taron cewa abin da aka kaddamar don rabawa kashi ashirin ne na hatsin da gwamnati ta saya yayin da za a yi rabon sauran a ma’auni daga baya a matakai.

Ya ce tuni aka aike da hatsin da ke tara a dukkanin kananan hukumomin 21 zuwa hedikwatar kananan hukumomin don raba wa ga al’ummar yankunan.

Daga karshe Kwamishinan ya bayyana irin kayan abincin da gwamnatin jihar ta sayo don rabawa ga watan azumin Ramadana sun hada da Gero, dawa da kuma shinkafa da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna NasirKebbirabon kayan abinciRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’adar Tashe A Kasar Hausa

Next Post

Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Aiwatar Da Haramcin Kamun Kifi Na Tsawon Shekaru 10 A Kogin Yangtze

Related

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya
Labarai

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

3 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

4 hours ago
Tsauraran Manufofin Tattalin ArziÆ™in Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana
Labarai

Tsauraran Manufofin Tattalin ArziÆ™in Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

5 hours ago
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
Labarai

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

17 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

21 hours ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

22 hours ago
Next Post
sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Aiwatar Da Haramcin Kamun Kifi Na Tsawon Shekaru 10 A Kogin Yangtze

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama ÆŠalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama ÆŠalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin ArziÆ™in Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin ArziÆ™in Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.