• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Abokan Hulɗa: NIS Ta Karrama Jami’anta Masu Aiki Tuƙuru

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
Ranar Abokan Hulɗa: NIS Ta Karrama Jami’anta Masu Aiki Tuƙuru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta karrama wasu jami’anta sakamakon bajinta da suka nuna wajen gudanar da aiki tuƙuru.

Hukumar NIS ta karrama jami’an ne a domin bikin ranar abokan hulɗa ta duniya ta 2022, da hukumar ta gudanar shalkwatarta da ke Abuja yau Juma’a, 7 ga watan Oktobar 2022.

  • Mauludi: Buhari Ya Bukaci ’Yan Siyasa Su Guje Wa Amfani Da Kalaman Batanci

Da yake jawabi yayin karramawar, shugaban hukumar ta NIS, CGI Isah Jere Idris ya bayyana cewa wannan babbar rana ce mai matuƙar muhimmanci ga hukumar ta NIS wajen gabatar da nasarori da ta cimma a lokacin gudanar da ayyukanta.

“Mun saba gudanar da murnar wannan rana wajen mayar da hankali kan abokan hulɗa wato mutanen da muke wa hidima. A duk lokacin da muka mayar da hankali wajen yi wa abokan hulɗa ayyukan da suka dace, to lallai za mu samu jinjina ta musamman daga gare su wanda zai ƙara mana zimmar yin aiki tuƙuru.

NIS
“Ya zama dole a wannan rana mu karrama wasu daga cikin jami’anmu waɗanda suka yi aiki tuƙuru duk da irin ƙalubale da muke fuskanta amma suka jajirce wajen gudanar da aiki yadda ya kamata. Mun ga ya kamata mu karrama su a daidai ranar da muke murnar abokan hulɗa ta duniya.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

“Wannan rana ta kasance kusan watanni 8 da muka yi biki makamancin haka a NIS a watan Fabrairun 2022, ga shi ya sake faɗowa a daidai wannan lokaci mai albarka.

NIS
“Ina da ajandoji guda uku waɗanda suka haɗa da kyautata jin daɗin jami’ai, kula da iyakokin ƙasa da kuma inganta ayyukan bayar da fasfo.

“A kan abubuwan da suka shafi jin daɗin jami’ai wanda muke murna a wannan rana kuwa, mun yi ƙoƙarin buɗe asusu na musamman domin tallafa wa iyalan jami’anmu waɗanda suka mutu a bakin aiki da kuma waɗanda suka yi ritaya. Haka kuma muna ƙoƙarin bai wa jami’anmu abubuwan da suke buƙata musamnman wajen biyan su haƙƙoƙinsu domin samun ingancin aiki.

NIS
“Tun lokacin da na karɓi ragamar shugabancin hukumar NIS, na gaji basussuka na biliyoyin nairori. Bayan na tattauna da mahukunta, mun miƙa ƙuduri ga gwamnati ta hanyar ma’aikatar da take kula da ayyukanmu domin ƙarin kuɗaɗe da zai ba mu damar biyan bashi. Ina fatan za mu samu nasarar amincewa da buƙatarmu.

“Mun kasance muna da tsarin karrama jami’anmu waɗanda suke aiki tuƙuru domin ƙara musu ƙwarin gwiwa wajen gudanar da aiki yadda ya dace. Wannan karramawa ta kasance yabo da jinjina ga jami’ai wajen ƙara jajircewar gudanar da aiki a hukumar NIS.

NIS
“A irin wannan biki da muka gudanar a watan Fabrairu, mun samu nasarar karrama jami’ai guda 30 bisa gudanar da aiki tuƙuru. Amma a wannan karon jami’ai 8 kaɗai muka karrama domin yaba musu kan gudummuwar da suka bayar na gudanar da aiki yadda ya kamata.”

NIS
Ya ƙara da cewa hukumar NIS tana alfahari da dukkan jami’anta wajen ƙoƙarin yi wa ‘Yan Nijeriya ayyukan da suke buƙata. Ya ce bisa ƙoƙarin jami’an ne ma ya sa sau uku bi-da-bi hukumar tana zama gwarzuwa da ta lashe kambi a tsakanin ma’aikatun gwamnati. Ya ce da wannan ne yake jinjina da dukkan jami’ai da suke zama silar nasarar da hukumar ke samu wajen zama ta ɗaya.

A cewarsa, hukumar ta NIS za ta ci gaba da zage damtse wajen gudanar da ayyukanta cikin tsari da ƙwarewa domin yi wa ‘yan Nijeriya ayyukan da suke buƙata ba tare da wata matsala ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Yi Nazarin Hukuncin Kotun Daukaka Kara – ASUU

Next Post

Bukatar ‘Yan Siyasa Su San Kalaman Da Za Su Furta Lokacin Kamfen

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

1 hour ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

2 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

3 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

5 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

6 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

7 hours ago
Next Post
Bukatar ‘Yan Siyasa Su San Kalaman Da Za Su Furta Lokacin Kamfen

Bukatar ‘Yan Siyasa Su San Kalaman Da Za Su Furta Lokacin Kamfen

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.