ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Abokan Hulɗa: NIS Ta Karrama Jami’anta Masu Aiki Tuƙuru

by yahuzajere
4 years ago
NIS

Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta karrama wasu jami’anta sakamakon bajinta da suka nuna wajen gudanar da aiki tuƙuru.

Hukumar NIS ta karrama jami’an ne a domin bikin ranar abokan hulɗa ta duniya ta 2022, da hukumar ta gudanar shalkwatarta da ke Abuja yau Juma’a, 7 ga watan Oktobar 2022.

  • Mauludi: Buhari Ya Bukaci ’Yan Siyasa Su Guje Wa Amfani Da Kalaman Batanci

Da yake jawabi yayin karramawar, shugaban hukumar ta NIS, CGI Isah Jere Idris ya bayyana cewa wannan babbar rana ce mai matuƙar muhimmanci ga hukumar ta NIS wajen gabatar da nasarori da ta cimma a lokacin gudanar da ayyukanta.

ADVERTISEMENT

“Mun saba gudanar da murnar wannan rana wajen mayar da hankali kan abokan hulɗa wato mutanen da muke wa hidima. A duk lokacin da muka mayar da hankali wajen yi wa abokan hulɗa ayyukan da suka dace, to lallai za mu samu jinjina ta musamman daga gare su wanda zai ƙara mana zimmar yin aiki tuƙuru.

NIS
“Ya zama dole a wannan rana mu karrama wasu daga cikin jami’anmu waɗanda suka yi aiki tuƙuru duk da irin ƙalubale da muke fuskanta amma suka jajirce wajen gudanar da aiki yadda ya kamata. Mun ga ya kamata mu karrama su a daidai ranar da muke murnar abokan hulɗa ta duniya.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

“Wannan rana ta kasance kusan watanni 8 da muka yi biki makamancin haka a NIS a watan Fabrairun 2022, ga shi ya sake faɗowa a daidai wannan lokaci mai albarka.

NIS
“Ina da ajandoji guda uku waɗanda suka haɗa da kyautata jin daɗin jami’ai, kula da iyakokin ƙasa da kuma inganta ayyukan bayar da fasfo.

“A kan abubuwan da suka shafi jin daɗin jami’ai wanda muke murna a wannan rana kuwa, mun yi ƙoƙarin buɗe asusu na musamman domin tallafa wa iyalan jami’anmu waɗanda suka mutu a bakin aiki da kuma waɗanda suka yi ritaya. Haka kuma muna ƙoƙarin bai wa jami’anmu abubuwan da suke buƙata musamnman wajen biyan su haƙƙoƙinsu domin samun ingancin aiki.

NIS
“Tun lokacin da na karɓi ragamar shugabancin hukumar NIS, na gaji basussuka na biliyoyin nairori. Bayan na tattauna da mahukunta, mun miƙa ƙuduri ga gwamnati ta hanyar ma’aikatar da take kula da ayyukanmu domin ƙarin kuɗaɗe da zai ba mu damar biyan bashi. Ina fatan za mu samu nasarar amincewa da buƙatarmu.

“Mun kasance muna da tsarin karrama jami’anmu waɗanda suke aiki tuƙuru domin ƙara musu ƙwarin gwiwa wajen gudanar da aiki yadda ya dace. Wannan karramawa ta kasance yabo da jinjina ga jami’ai wajen ƙara jajircewar gudanar da aiki a hukumar NIS.

NIS
“A irin wannan biki da muka gudanar a watan Fabrairu, mun samu nasarar karrama jami’ai guda 30 bisa gudanar da aiki tuƙuru. Amma a wannan karon jami’ai 8 kaɗai muka karrama domin yaba musu kan gudummuwar da suka bayar na gudanar da aiki yadda ya kamata.”

NIS
Ya ƙara da cewa hukumar NIS tana alfahari da dukkan jami’anta wajen ƙoƙarin yi wa ‘Yan Nijeriya ayyukan da suke buƙata. Ya ce bisa ƙoƙarin jami’an ne ma ya sa sau uku bi-da-bi hukumar tana zama gwarzuwa da ta lashe kambi a tsakanin ma’aikatun gwamnati. Ya ce da wannan ne yake jinjina da dukkan jami’ai da suke zama silar nasarar da hukumar ke samu wajen zama ta ɗaya.

A cewarsa, hukumar ta NIS za ta ci gaba da zage damtse wajen gudanar da ayyukanta cikin tsari da ƙwarewa domin yi wa ‘yan Nijeriya ayyukan da suke buƙata ba tare da wata matsala ba.

NIS
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Bukatar ‘Yan Siyasa Su San Kalaman Da Za Su Furta Lokacin Kamfen

Bukatar ‘Yan Siyasa Su San Kalaman Da Za Su Furta Lokacin Kamfen

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.