ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Malamai ta Duniya: Aikin Malanta A Zamanin Nan A Nijeriya 

by Sadiq
3 years ago
Malamai

Ranar 5 ga watan Oktoba na kowace shekara ita ce ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin yin bikin ranar malamai ta duniya.

An ware ranar don nuna girmamawa da kuma karrama su kan irin namijin kokarin da suke yi wajen ilimantarwa da kuma bai wa yara tarbiyya.

  • Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4
  • Atiku Ya Karbi Mutane Dubu 25 Da Suka Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP A Bauchi

Taken bikin ranar na wannan shekarar shi ne: Mafita da hanyoyin inganta rayuwar malamai.

ADVERTISEMENT

Sai dai a wannan lokaci Leadership Hausa, ta cikin shirin ‘Twitter Space’ da yi, ta zanta da wasu masana kan yadda aikin malamanta yake a da, da kuma yanzu.

Sannan kai tsaye a cikin shirin na kafar Twitter sauran jama’a sun bayyana ra’ayoyinsu kan yadda aikin yake da kuma irin hobbasa da suke ganin malamai na bukata da ma shi kansa ilimin.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Daya daga cikin wadanda suka tsinkayin shirin, mai suna El-Faruk, ya ce akwai bukatar yi wa malamai adashin gata don samun nutsuwar gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

“Malami yana da abubuwa da dama da za su taimaka masa don bunkasa ilimi. Ma’ana dole ne gwamnati ta inganta aikin malamai da kula yanayin kula da su.

“Sannan a matsayinmu na dalibai yana da kyau muke waiwayar malamanmu walau na Firamare, Sakandare ko kuma na tsangaya, saboda da yawan irin wadannan malamai na fama da yanayin rayuwa saboda halin rayuwa da kasar nan ta tsinci kanta a ciki.

“Mu kyautata musu ko mu dauki karatun wasu daga cikin ‘ya’yansu,” a cewar El-Faruk.

Shi kuwa Abdul Rahman, cewa ya yi akwai bukatar iyaye da dalibai su san darajar malamai.

“Iyaye da dalibai ya kamata su san darajar malamai, saboda wasu sha’awa ga aikin ce tasa suke yi, sai dai wasu na musu kallon kaskanci wanda hakan ya sa ake yi wa fagen kallon hadarin-kaji.”

Wani abu daga cikin hanyoyin walwala da aka yi wa malamai shi ne, kara wa’adin ritaya na malaman, wato daga shekara 60 zuwa 65, sannan gwamnatin tarayya ta yi alkawarin ingata wasu abubuwa da suka shafi albashi da alawus-alawus nasu.

Kazalika, an kalli irin badakalar da ake tafkawa a bangaren aikin malamanta wanda suka lalata da dalibai musamman mata a wasu lokutan ma har da maza, lalata don neman maki.

Wasu sun ce duk da cewar akwai malaman da ake samu da irin wadannan laifuka, amma wani kaulin daliban matan ne ke kai kan su don yin lalata da su don cimma bukatarsu musamman wajen ganin sun ci jarabawa da sauransu.

Amma wasu na ganin gudunmawar da suke bayarwa, ita ce abin da ya kamata jama’a su fi mayar da hankali, saboda girman abin da suke yi ya fi karfin auna shi a ma’auni.

Amma, gwamnati ta tanadi hukunci ga baragurbin malamai da aka samu da irin wannan laifi.

Matsalolin da ke tattare da harkar ilimi a Nijeriya na da tarin yawa, akwai karancin malamai, karancin walwalar malamai, cunkoson dalibai a azuzuwa, karancin albashi da sauran tarin matsaloli.

Mutane da dama sun bada gudunmawa ta hanyar kira ga gwamnatoci daga kowane mataki da masu ruwa da tsaki da masu hannu da shuni da su taimaki harkar ilimi don samar da manyan gobe masu hikima, da za su saita wannan kasa a nan gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
An Cafke Wani Mutum Da Ya Yi Wa ‘Yar Uwarsa Mara Hankali Fyade A Kebbi 

An Cafke Wani Mutum Da Ya Yi Wa 'Yar Uwarsa Mara Hankali Fyade A Kebbi 

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.