• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Malamai ta Duniya: Aikin Malanta A Zamanin Nan A Nijeriya 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Ranar Malamai ta Duniya: Aikin Malanta A Zamanin Nan A Nijeriya 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 5 ga watan Oktoba na kowace shekara ita ce ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin yin bikin ranar malamai ta duniya.

An ware ranar don nuna girmamawa da kuma karrama su kan irin namijin kokarin da suke yi wajen ilimantarwa da kuma bai wa yara tarbiyya.

  • Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4
  • Atiku Ya Karbi Mutane Dubu 25 Da Suka Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP A Bauchi

Taken bikin ranar na wannan shekarar shi ne: Mafita da hanyoyin inganta rayuwar malamai.

Sai dai a wannan lokaci Leadership Hausa, ta cikin shirin ‘Twitter Space’ da yi, ta zanta da wasu masana kan yadda aikin malamanta yake a da, da kuma yanzu.

Sannan kai tsaye a cikin shirin na kafar Twitter sauran jama’a sun bayyana ra’ayoyinsu kan yadda aikin yake da kuma irin hobbasa da suke ganin malamai na bukata da ma shi kansa ilimin.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Daya daga cikin wadanda suka tsinkayin shirin, mai suna El-Faruk, ya ce akwai bukatar yi wa malamai adashin gata don samun nutsuwar gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

“Malami yana da abubuwa da dama da za su taimaka masa don bunkasa ilimi. Ma’ana dole ne gwamnati ta inganta aikin malamai da kula yanayin kula da su.

“Sannan a matsayinmu na dalibai yana da kyau muke waiwayar malamanmu walau na Firamare, Sakandare ko kuma na tsangaya, saboda da yawan irin wadannan malamai na fama da yanayin rayuwa saboda halin rayuwa da kasar nan ta tsinci kanta a ciki.

“Mu kyautata musu ko mu dauki karatun wasu daga cikin ‘ya’yansu,” a cewar El-Faruk.

Shi kuwa Abdul Rahman, cewa ya yi akwai bukatar iyaye da dalibai su san darajar malamai.

“Iyaye da dalibai ya kamata su san darajar malamai, saboda wasu sha’awa ga aikin ce tasa suke yi, sai dai wasu na musu kallon kaskanci wanda hakan ya sa ake yi wa fagen kallon hadarin-kaji.”

Wani abu daga cikin hanyoyin walwala da aka yi wa malamai shi ne, kara wa’adin ritaya na malaman, wato daga shekara 60 zuwa 65, sannan gwamnatin tarayya ta yi alkawarin ingata wasu abubuwa da suka shafi albashi da alawus-alawus nasu.

Kazalika, an kalli irin badakalar da ake tafkawa a bangaren aikin malamanta wanda suka lalata da dalibai musamman mata a wasu lokutan ma har da maza, lalata don neman maki.

Wasu sun ce duk da cewar akwai malaman da ake samu da irin wadannan laifuka, amma wani kaulin daliban matan ne ke kai kan su don yin lalata da su don cimma bukatarsu musamman wajen ganin sun ci jarabawa da sauransu.

Amma wasu na ganin gudunmawar da suke bayarwa, ita ce abin da ya kamata jama’a su fi mayar da hankali, saboda girman abin da suke yi ya fi karfin auna shi a ma’auni.

Amma, gwamnati ta tanadi hukunci ga baragurbin malamai da aka samu da irin wannan laifi.

Matsalolin da ke tattare da harkar ilimi a Nijeriya na da tarin yawa, akwai karancin malamai, karancin walwalar malamai, cunkoson dalibai a azuzuwa, karancin albashi da sauran tarin matsaloli.

Mutane da dama sun bada gudunmawa ta hanyar kira ga gwamnatoci daga kowane mataki da masu ruwa da tsaki da masu hannu da shuni da su taimaki harkar ilimi don samar da manyan gobe masu hikima, da za su saita wannan kasa a nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaiIlimiMalamaiMalantaRanar Malamai ta Duniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

Next Post

An Cafke Wani Mutum Da Ya Yi Wa ‘Yar Uwarsa Mara Hankali Fyade A Kebbi 

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

13 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 day ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
An Cafke Wani Mutum Da Ya Yi Wa ‘Yar Uwarsa Mara Hankali Fyade A Kebbi 

An Cafke Wani Mutum Da Ya Yi Wa 'Yar Uwarsa Mara Hankali Fyade A Kebbi 

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.