• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Malamai ta Duniya: Aikin Malanta A Zamanin Nan A Nijeriya 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Ranar Malamai ta Duniya: Aikin Malanta A Zamanin Nan A Nijeriya 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 5 ga watan Oktoba na kowace shekara ita ce ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin yin bikin ranar malamai ta duniya.

An ware ranar don nuna girmamawa da kuma karrama su kan irin namijin kokarin da suke yi wajen ilimantarwa da kuma bai wa yara tarbiyya.

  • Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4
  • Atiku Ya Karbi Mutane Dubu 25 Da Suka Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP A Bauchi

Taken bikin ranar na wannan shekarar shi ne: Mafita da hanyoyin inganta rayuwar malamai.

Sai dai a wannan lokaci Leadership Hausa, ta cikin shirin ‘Twitter Space’ da yi, ta zanta da wasu masana kan yadda aikin malamanta yake a da, da kuma yanzu.

Sannan kai tsaye a cikin shirin na kafar Twitter sauran jama’a sun bayyana ra’ayoyinsu kan yadda aikin yake da kuma irin hobbasa da suke ganin malamai na bukata da ma shi kansa ilimin.

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Daya daga cikin wadanda suka tsinkayin shirin, mai suna El-Faruk, ya ce akwai bukatar yi wa malamai adashin gata don samun nutsuwar gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

“Malami yana da abubuwa da dama da za su taimaka masa don bunkasa ilimi. Ma’ana dole ne gwamnati ta inganta aikin malamai da kula yanayin kula da su.

“Sannan a matsayinmu na dalibai yana da kyau muke waiwayar malamanmu walau na Firamare, Sakandare ko kuma na tsangaya, saboda da yawan irin wadannan malamai na fama da yanayin rayuwa saboda halin rayuwa da kasar nan ta tsinci kanta a ciki.

“Mu kyautata musu ko mu dauki karatun wasu daga cikin ‘ya’yansu,” a cewar El-Faruk.

Shi kuwa Abdul Rahman, cewa ya yi akwai bukatar iyaye da dalibai su san darajar malamai.

“Iyaye da dalibai ya kamata su san darajar malamai, saboda wasu sha’awa ga aikin ce tasa suke yi, sai dai wasu na musu kallon kaskanci wanda hakan ya sa ake yi wa fagen kallon hadarin-kaji.”

Wani abu daga cikin hanyoyin walwala da aka yi wa malamai shi ne, kara wa’adin ritaya na malaman, wato daga shekara 60 zuwa 65, sannan gwamnatin tarayya ta yi alkawarin ingata wasu abubuwa da suka shafi albashi da alawus-alawus nasu.

Kazalika, an kalli irin badakalar da ake tafkawa a bangaren aikin malamanta wanda suka lalata da dalibai musamman mata a wasu lokutan ma har da maza, lalata don neman maki.

Wasu sun ce duk da cewar akwai malaman da ake samu da irin wadannan laifuka, amma wani kaulin daliban matan ne ke kai kan su don yin lalata da su don cimma bukatarsu musamman wajen ganin sun ci jarabawa da sauransu.

Amma wasu na ganin gudunmawar da suke bayarwa, ita ce abin da ya kamata jama’a su fi mayar da hankali, saboda girman abin da suke yi ya fi karfin auna shi a ma’auni.

Amma, gwamnati ta tanadi hukunci ga baragurbin malamai da aka samu da irin wannan laifi.

Matsalolin da ke tattare da harkar ilimi a Nijeriya na da tarin yawa, akwai karancin malamai, karancin walwalar malamai, cunkoson dalibai a azuzuwa, karancin albashi da sauran tarin matsaloli.

Mutane da dama sun bada gudunmawa ta hanyar kira ga gwamnatoci daga kowane mataki da masu ruwa da tsaki da masu hannu da shuni da su taimaki harkar ilimi don samar da manyan gobe masu hikima, da za su saita wannan kasa a nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaiIlimiMalamaiMalantaRanar Malamai ta Duniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

Next Post

An Cafke Wani Mutum Da Ya Yi Wa ‘Yar Uwarsa Mara Hankali Fyade A Kebbi 

Related

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

4 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

1 day ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

1 day ago
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

1 day ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

1 day ago
Next Post
An Cafke Wani Mutum Da Ya Yi Wa ‘Yar Uwarsa Mara Hankali Fyade A Kebbi 

An Cafke Wani Mutum Da Ya Yi Wa 'Yar Uwarsa Mara Hankali Fyade A Kebbi 

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.