• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar ‘Yanci: ‘Yan Nijeriya Mazauna Landan Sun Nemi A Yi Wa Gwamnatin NNPP Adalci A Kano

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
NNPP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani ɓangare na murnar zagayowar Ranar Samun ‘Yanci shekaru 63 da Najeriya ta yi, ‘yan ƙasar mazauna Landan sun yi dafifi a Ofishin Jakadancin Najeriya da ke birnin Landan, inda su ka nemi a yi adalci a shari’ar zaɓen gwamnan Kano.

Sun taru a ofishin kowane ɗauke da kwali mai ɗauke da bayanan zargin cewa jam’iyyar APC a ƙarƙashin jagorancin tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje ta yi katsalandan a shari’ar da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Kano ta yanke.

  • Trump Ya Bayyana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Laifin Zamba
  • Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Mutum Hudu A Taraba

Sun riƙa ɗaga kwalaye masu ɗauke rubutu daban-daban, domin su isar da saƙon neman a yi shari’a bisa tsari na gaskiya tare da adalci ga gwamnatin NNPP a Jihar Kano.

Sun taru ne a ranar Lahadi, ranar da ta yi daidai da ranar zagayowar samun ‘yancin Najeriya.

Wasu daga cikin saƙonnin da ke rubuce a kwalayen sun haɗa da:

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

“Yancin kowace ƙasa dai ya dogara ne ga ‘yancin fannin shari’ar ta.”

“Kada fa a yi wa Kano fashi da ƙwacen mulki. Tinubu ya bari tsarin mulki da shari’a mai adalci ta wanzu a Kano, kuma ta yi tasiri a hukunci.”

“Tilas A Bar Wa Kano Abin Da Suka zaɓa, Ba Sauran Mulkin Rashin Adalci:Kada a sake a yi wa Abba ƙwacen nasarar zaɓen da ya yi.”

“Dole Ne Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe Su Yi Adalci – kuma kada shari’ar zaɓen Kano ta zama zakaran-gwajin-dafin zalunci.”

“A Nesanta Siyasa Daga Cikin Kotunan Mu – Kotun Ɗaukaka Ƙarar Zaɓen Kano Ta Bi Son Ran Wasu!”

“Rashin nuna ɓangaranci ga masu shari’a shi ne jigon yanke hukunci. Kanawa sun cancanci a yi masu adalci da gaskiya, ba a siyasantar da hukuncin kotun zaɓe ba.”

“A Kare Dimokraɗiyya kuma a yi adalci a kotunan shari’un zaɓe. Kanawa sun cancanci a yi masu adalci.”

NNPP

Jagoran masu jerin gwanon zanga-zangar, Dakta Aminu Bello, ya shaida wa ‘yan jarida cewa sun je Ofishin Jakadancin Najeriya da ke birnin Landan ne domin nuna rashin amincewa da hukuncin da Kotun Shari’ar Zaɓen Gwamnan Jihar Kano ta yanke, wanda ya haifar da matuƙar damuwa kan rashin adalcin da ake zargin an yi. Lamarin da ya haifar da kiraye-kirayen a yi gaskiya da adalci a Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Tarayya.

Bello ya ce hukuncin da Kotun Shari’ar Zaɓen Kano ta yanke ya jefa shakku a kan fa’ida da nagartar da ake tinƙahon samu a tsarin dimokraɗiyya.

Ya ce lallai kada a sake a ƙwace halastacciyar nasarar da Gwamna Abba Kabir Yusuf na NNPP ya samu.

A ƙarshe ya yi kira ga ƙungiyoyin kare haƙƙi da na dimokraɗiyya, jam’iyyun siyasa da ƙungiyoyin ƙasa-da-ƙasa su sa ido sosai a kan abin da ke faruwa a Kano.

“Kuma muna kira ga hukuma ta yi ƙwaƙƙwaran bincike tare da sake bibiyar yadda aka zartas da hukuncin shari’ar zaɓen gwamna a Kano, tare da hukunta duk alƙalin da aka samu ya bada kai borin wasu masu son shirya zalunci ya hau,” Inji Bello.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kotun ZabeKwankwasiyyaNNPP
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Kasuwa 40 Sun Rasu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

Next Post

Tinubu Ya Maye Sunan El-Rufai, Ya Aike Wa Majalisa Karin Sunan Ministoci

Related

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

39 minutes ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

4 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

6 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

9 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

10 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

13 hours ago
Next Post
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata

Tinubu Ya Maye Sunan El-Rufai, Ya Aike Wa Majalisa Karin Sunan Ministoci

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.