• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Kulawa Da Jama’a Ba Dimokuradiyya Ba Ce

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Rashin Kulawa Da Jama’a Ba Dimokuradiyya Ba Ce
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutanen duniya na kallon kasar Amurka a matsayin wata babbar kasa, wadda ke kan gaba a fannin tattalin arziki, da na ingancin aikin likitanci.

Sai dai kasar ta fi shan kaye a fannin tinakar cutar COVID-19 a duniya, ganin yadda mutanen kasar miliyan 94.6 suka kamu da cutar, kana wasu miliyan 1.04 daga cikinsu suka mutu sakamakon cutar, inda suka kasance kimanin kashi 1 bisa kashi 6 na adadin duniya baki daya.

  • Sassauta Matakan Kandagarkin Cutar COVID-19 A Amurka Ya Haifar Da Mumunan Tasiri

Sai dai kasar ta sake gyaran manufarta a fannin tinkarar annobar COVID-19 a kwanan baya, inda ta fara dakatar da samar da na’urorin gwajin kwayoyin cuta kyauta daga ranar 2 ga watan Satumban da muke ciki, kana gwamnatin kasar za ta daina biyan kudin jinyar mutanen da suka kamu da cutar, da na yi wa mutanen kasar allurar rigakafi, maimakon haka za a dora nauyin kan kamfanonin ishora da jama’ar kasar.

Duk da cewa kasar na ci gaba da fama da yanayi mai tsanani ta fuskar tinkarar cutar COVID-19.

An ce a makon da ya gabata, an samu karin mutane fiye da 85274 dake kamuwa da cutar COVID-19 da kimanin wasu 500 da suka mutu sakamakon cutar a kasar a kowace rana.

Labarai Masu Nasaba

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

To, ina dalilin da ya sa kasar Amurka ke ci gaba da saukaka matakan tinkarar annoba, yayin da yanayin cutar ke kara tsananta a kasar?
Da farko, gwamnatin kasar Amurka na fama da matsalar karancin kudi.
Bayan barkewar annobar COVID-19, gwamnatin kasar Amurka ta sha cin bashi da yawa, don daukar matakan tinkarar annoba, da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki. Sai dai matakin ya haddasa hauhawar farashin kayayyaki, da ba jama’a wahalar zaman rayuwa.

Zuwa yanzu,gwamnatin Joe Biden na neman rage kudin da hukumomin kasar ke kashewa, da takaita hauhawar farashin kaya, lamarin da ya sa ake fama da karancin kudi a ayyuka daban daban, ciki har da aikin tinkarar annoba.

Na biyu, shi ne, gogayar da jam’iyyun siysan kasar Amurka suke yi ta hana zuba jari ga aikin kandagarkin yaduwar annoba. Bayan gwamnatin kasar ta ce ana fama da matsalar karancin kudi na tinkarar annoba, nan take su ‘yan majalissun da suka kasance ‘ya’yan jam’iyyar Republican ta kasar suka fara zargin White House da yin karya. Daga baya aka hana zuba karin jari ga aikin tinkarar annoba.

Sa’an nan dalili na uku wanda ya fi muhimmanci shi ne, a ganin wasu ‘yan siyasan kasar Amurka, aikin kare lafiyar jama’ar kasar ba shi da muhimmanci, idan an kwatanta shi da aikin kasar na neman yin babakere a duniya, da yada tunanin Dimokuradiya irin na kasar.

A watan Maris na bana, an zartas da kasafin kudi da darajarsa ta kai dalar Amurka triliyan 1.5 a majalissun dokokin kasar Amurka.

Sai dai a cikin kundin kasafin kudin, an soke shiri na dala biliyan 15.6 na tallafawa kokarin tinkarar cutar COVID-19 sakamakon sabanin ra’ayin da ake samu tsakanin jam’iyyun siyasa na kasar, kana a maimakonsa an zartas da kudin tallafi na dala biliyan 13.6 da za a ba kasar Ukraine.

Yanzu haka majalissun dokokin kasar Amurka sun riga sun amince da tallafi na dala biliyan 50 da ake neman baiwa kasar ta Ukraine.

Wannan ya nuna cewa, idan tana so, kasar Amurka za ta iya samun kudin da take bukata wajen tinkarar annoba. Sai dai a idanun ‘yan siyasan kasar, aikin yayyata tunanin Dimokuradiya irin na kasar Amurka ya fi muhimmanci.

Sanin kowa ne, kafin a ce wata kasa mai tsari na dimokuradiya ne, ya kamata a duba manufofinta na taimakawa kare moriyar jama’a.

Yadda kasar Amurka ta zuba kudi ga Ukraine, ya taimaki ‘yan siyasan kasar cimma burinsu na tabbatar da yin babakere a duniya, da fitar da tunanin Dimokuradiya irin na kasar Amurka. Haka kuma ya sa kamfanonin kera makamai na kasar cin riba sosai.

Sa’an nan bayan da gwamnatin kasar Amurka ta mika aikin kare jama’a daga annoba ga kasuwa, su kamfanonin samar da magunguna da masu ba da hidimar jinya za su samu makudan kudi. Sai dai an kasa kula da wasu.

Saboda har yanzu a kasar Amurka akwai kimanin mutane miliyan 30 da ba su iya sayen hidimar inshorar lafiya ba. Daina samar da hidimomi kyauta na nufin za a kyale lafiya da tsaron wadannan mutane marasa karfi. Ga ta nan dai, wata kasar da ta kasa kulawa da jama’arta, har ma tana so a dinga kallonta a matsayin mai jagorantar aikin raya dimokuradiya.

Yadda gwamnatin kasar Amurka ta kasa sauke nauyin dake bisa wuyanta na tinkarar annobar COVID-19 ya sa jama’ar kasar shan wahala sosai.

A sa’i daya kuma, ya sa mutanen duniya fahimtar cewa alkawarinta na kare dimokuradiya a duniya ba shi da gaskiya, saboda Rashin kulawa da jama’a ba dimokuradiya ba ce. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Samu Tiriliyan N1.18 Daga Kudaden Haraji A Wata 6

Next Post

Da Dumi-dumi: Liz Truss Ce Sabuwar Fira Ministar Burtaniya

Related

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

14 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

15 hours ago
Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu
Daga Birnin Sin

Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

16 hours ago
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

1 day ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

2 days ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

2 days ago
Next Post
Da Dumi-dumi: Liz Truss Ce Sabuwar Fira Ministar Burtaniya

Da Dumi-dumi: Liz Truss Ce Sabuwar Fira Ministar Burtaniya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

August 11, 2025
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

August 11, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

August 11, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.