• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Gamayyar Kungiyoyin Farar Hula Za Su Yi Addu’o’i Na Musamman A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Rashin Tsaro

Gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Katsina sun kafu matuka saboda karuwar hare-haren ‘yan bindiga a wasu garuruwa da ke nuna halin ko in kula da gwamnatin ke yi wa harkar tsaro.

Wanda har yanzu ta kasa kawo karshen kisan da ake yi wa wadanda ba su ji ba, ba su gani ba.

  • Ya Kamata ‘Yan Nijeriya Su Yi Hattara Da Atiku – Magoya Bayan Tinubu
  • Gwamnatin Kaduna Ta Ba Da Hutun Kwana 3 Don Jama’a Su Yi Rijistar Katin Zabe

Bayanan hakan yana kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Katsina, Abdulrahaman Abdullahi Dutsima, ya sanya wa hannu ya kuma raba wa manema labarai a Katsina.

Sanarwar ta ce ayyukan ‘yan ta’adda sun kai wani mataki da kullum sai an kai harin wuce gona da iri, saboda yadda ‘yan bindigar ke sayen makaman kare dangi da kudaden da ake biyansu, bayan sun dauke jama’a, sannan hakan na kara masu karfi ta yadda suke kara fadada kai hare-haren ba ji ba gani.

“Jihar Katsina a yau ta koma wani wuri na rashin tabbas a rayuwa babu waje buya kuma babu wanda ya tsira, hatta kokuwar Katsina tana fuskantar barazana, inda sha’anin samar da tsaron dukiya da rayukan al’umma ya zama abu na farko da shuwagabanni ya kamata su yi kafin wani abu, amma abin takaici babu wata hubbasa daga bangaren gwamnati na tunkarar wannan matsala.

LABARAI MASU NASABA

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

Haka kuma sanarwa ta kara da cewa yanzu babu abin da ya rage sai a koma ga Allah ta hanyar yin addu’o’in neman gafarar Allah tunda duk kira da jan hankali da rubuce-rubucen an riga an yi domin jan hankalin gwamanti a kan matsalar tsaro amma shiru kake ji kamar an aiki bawa garinsu, zabin da rage shi ne addu’o’i.

Abdullahi, ya ce a matsayinsu na ‘yan Adam mun san cewa mulki na Allah ne kuma shi kadai ne zai yi maganin wannan matsala fiye da tunani.

Ya ce za a ci gaba da yin wadannan addu’o’i ne a masallatai da kuma majami’u da makarantun islamiyya da na allo a duk fadin jihar Katsina.

Daga karshe gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Katsina na mika sakon ta’aziyarsu da jaje ga ‘yan uwan wadanda suka rasa ransu a sakamakon ayyukan ‘yan bindiga.

Sannan sun yin addu’ar Allah ya kawo karshen wannan mummunan yanayi da al’umma ta tsinci kanta a ciki, ya maido mata da zaman lafiya a jihar Katsina da kasa baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa
Labarai

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina
Labarai

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Next Post
Hukumomi Sun Tsare Mahaifin Da Ya Sayar Da ‘Ya’Yansa Zabiya A Mozambique

Hukumomi Sun Tsare Mahaifin Da Ya Sayar Da 'Ya'Yansa Zabiya A Mozambique

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025
Tanka

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.