ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Gamayyar Kungiyoyin Farar Hula Za Su Yi Addu’o’i Na Musamman A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
Rashin Tsaro

Gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Katsina sun kafu matuka saboda karuwar hare-haren ‘yan bindiga a wasu garuruwa da ke nuna halin ko in kula da gwamnatin ke yi wa harkar tsaro.

Wanda har yanzu ta kasa kawo karshen kisan da ake yi wa wadanda ba su ji ba, ba su gani ba.

  • Ya Kamata ‘Yan Nijeriya Su Yi Hattara Da Atiku – Magoya Bayan Tinubu
  • Gwamnatin Kaduna Ta Ba Da Hutun Kwana 3 Don Jama’a Su Yi Rijistar Katin Zabe

Bayanan hakan yana kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Katsina, Abdulrahaman Abdullahi Dutsima, ya sanya wa hannu ya kuma raba wa manema labarai a Katsina.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce ayyukan ‘yan ta’adda sun kai wani mataki da kullum sai an kai harin wuce gona da iri, saboda yadda ‘yan bindigar ke sayen makaman kare dangi da kudaden da ake biyansu, bayan sun dauke jama’a, sannan hakan na kara masu karfi ta yadda suke kara fadada kai hare-haren ba ji ba gani.

“Jihar Katsina a yau ta koma wani wuri na rashin tabbas a rayuwa babu waje buya kuma babu wanda ya tsira, hatta kokuwar Katsina tana fuskantar barazana, inda sha’anin samar da tsaron dukiya da rayukan al’umma ya zama abu na farko da shuwagabanni ya kamata su yi kafin wani abu, amma abin takaici babu wata hubbasa daga bangaren gwamnati na tunkarar wannan matsala.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

Haka kuma sanarwa ta kara da cewa yanzu babu abin da ya rage sai a koma ga Allah ta hanyar yin addu’o’in neman gafarar Allah tunda duk kira da jan hankali da rubuce-rubucen an riga an yi domin jan hankalin gwamanti a kan matsalar tsaro amma shiru kake ji kamar an aiki bawa garinsu, zabin da rage shi ne addu’o’i.

Abdullahi, ya ce a matsayinsu na ‘yan Adam mun san cewa mulki na Allah ne kuma shi kadai ne zai yi maganin wannan matsala fiye da tunani.

Ya ce za a ci gaba da yin wadannan addu’o’i ne a masallatai da kuma majami’u da makarantun islamiyya da na allo a duk fadin jihar Katsina.

Daga karshe gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Katsina na mika sakon ta’aziyarsu da jaje ga ‘yan uwan wadanda suka rasa ransu a sakamakon ayyukan ‘yan bindiga.

Sannan sun yin addu’ar Allah ya kawo karshen wannan mummunan yanayi da al’umma ta tsinci kanta a ciki, ya maido mata da zaman lafiya a jihar Katsina da kasa baki daya.

Rashin Tsaro
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Next Post
Hukumomi Sun Tsare Mahaifin Da Ya Sayar Da ‘Ya’Yansa Zabiya A Mozambique

Hukumomi Sun Tsare Mahaifin Da Ya Sayar Da 'Ya'Yansa Zabiya A Mozambique

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.