ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Gamayyar Kungiyoyin Farar Hula Za Su Yi Addu’o’i Na Musamman A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
Rashin Tsaro

Gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Katsina sun kafu matuka saboda karuwar hare-haren ‘yan bindiga a wasu garuruwa da ke nuna halin ko in kula da gwamnatin ke yi wa harkar tsaro.

Wanda har yanzu ta kasa kawo karshen kisan da ake yi wa wadanda ba su ji ba, ba su gani ba.

  • Ya Kamata ‘Yan Nijeriya Su Yi Hattara Da Atiku – Magoya Bayan Tinubu
  • Gwamnatin Kaduna Ta Ba Da Hutun Kwana 3 Don Jama’a Su Yi Rijistar Katin Zabe

Bayanan hakan yana kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Katsina, Abdulrahaman Abdullahi Dutsima, ya sanya wa hannu ya kuma raba wa manema labarai a Katsina.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce ayyukan ‘yan ta’adda sun kai wani mataki da kullum sai an kai harin wuce gona da iri, saboda yadda ‘yan bindigar ke sayen makaman kare dangi da kudaden da ake biyansu, bayan sun dauke jama’a, sannan hakan na kara masu karfi ta yadda suke kara fadada kai hare-haren ba ji ba gani.

“Jihar Katsina a yau ta koma wani wuri na rashin tabbas a rayuwa babu waje buya kuma babu wanda ya tsira, hatta kokuwar Katsina tana fuskantar barazana, inda sha’anin samar da tsaron dukiya da rayukan al’umma ya zama abu na farko da shuwagabanni ya kamata su yi kafin wani abu, amma abin takaici babu wata hubbasa daga bangaren gwamnati na tunkarar wannan matsala.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Haka kuma sanarwa ta kara da cewa yanzu babu abin da ya rage sai a koma ga Allah ta hanyar yin addu’o’in neman gafarar Allah tunda duk kira da jan hankali da rubuce-rubucen an riga an yi domin jan hankalin gwamanti a kan matsalar tsaro amma shiru kake ji kamar an aiki bawa garinsu, zabin da rage shi ne addu’o’i.

Abdullahi, ya ce a matsayinsu na ‘yan Adam mun san cewa mulki na Allah ne kuma shi kadai ne zai yi maganin wannan matsala fiye da tunani.

Ya ce za a ci gaba da yin wadannan addu’o’i ne a masallatai da kuma majami’u da makarantun islamiyya da na allo a duk fadin jihar Katsina.

Daga karshe gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Katsina na mika sakon ta’aziyarsu da jaje ga ‘yan uwan wadanda suka rasa ransu a sakamakon ayyukan ‘yan bindiga.

Sannan sun yin addu’ar Allah ya kawo karshen wannan mummunan yanayi da al’umma ta tsinci kanta a ciki, ya maido mata da zaman lafiya a jihar Katsina da kasa baki daya.

Rashin Tsaro
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Hukumomi Sun Tsare Mahaifin Da Ya Sayar Da ‘Ya’Yansa Zabiya A Mozambique

Hukumomi Sun Tsare Mahaifin Da Ya Sayar Da 'Ya'Yansa Zabiya A Mozambique

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.