A ranar Laraba ne daruruwan matasa suka tare hanyar Auchi-Igarra-Ibillo ta jihar Edo, domin nuna rashin amincewarsu da lalacewar hanyar da suka ce ta janyo yawaitar sace-sacen jama’a da rashin ababen more rayuwa.
Masu zanga-zangar sun yi korafin cewa, garkuwa da mutane ya zama ruwan dare a kullum saboda munanan hanyoyi da kuma rashin isassun ababen more rayuwa.
- Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho
- ‘Yansanda Sun Kama Matasa 2 Da Ake Zargi Da Satar Mota A Kebbi
Sun kuma yi tir da cewa, masu rike da mukaman siyasa daga yankin ba su damu da halin da jama’a ke ciki ba.
Zanga-zangar ta haifar da cunkoso a kan hanyar yayin da matafiya da suka hada da manyan motoci a kan titin suka tsaya cak na tsawon sa’o’i.
Matasan sun kuma koka da yadda har yanzu ba a sako wani jigo a jam’iyyar LP ba, Okasime Olowojoba da aka yi garkuwa da shi kusan wata guda duk da biyan sama da Naira miliyan 5 kudin fansa.
Daya daga cikin masu zanga-zangar Paul Lawani ya ce, “Ba za mu iya ci gaba da zama bayi a kasarmu ba, ya kamata gwamnati ta fada mana abin da take yi.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp