• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsoma Baki Ya Sa Kasar Sin Ke Samun Karin Abokai

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Rashin Tsoma Baki Ya Sa Kasar Sin Ke Samun Karin Abokai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping na ziyara a kasar Saudiyya, inda zai halarci taron koli na Sin da kasashen Larabawa, da taron kolin Sin da kwamitin kasashen dake dab da mashigin tekun Pasha ko (GCC). Yadda shugabannin kasashen Larabawa da dama suka taru a gu daya don tattauna harkokin hadin gwiwa tare da kasar Sin ya shaida matsayi mai muhimmanci na kasar Sin a idon kasashen.

Wannan muhimmin matsayi, tushensa shi ne cudanya da cinikin da Sin da kasashen Larabawa suka yi cikin shekaru fiye da 2000 da suka wuce, bi ta hanyar Siliki, da ma karfin tattalin arzikin Sin da ya zama na biyu a duniya, da huldar abota da ta shafi manyan tsare-tsare da kasashen Larabawa suka kulla da kasar Sin.

  • Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce

Haka zalika, a ganina, wani babban dalili na daban da ya sa kasashen Larabawa suke girmama kasar Sin, shi ne manufarta ta “rashin tsoma baki cikin harkokin gida na sauran kasashe”.

Wasu kafofin watsa labaru na kasashen yamma, wadanda ke son shafa wa kasar Sin bakin fenti, su kan bayyana manufar Sin ta rashin tsoma baki a matsayin “rashin daukar nauyi”, ko kuma “rashin niyyar tabbatar da adalci”. Amma hakika Sin na daukar wannan manufa ne da zummar girmama ikon mulki na sauran kasashe, da amincewa da matsayinsu na daya da na kasar Sin. Wannan girmamawa, da zaman daidai wadaida, su ne abubuwan da kasashen Larabawa suka kasa samu, yayin da suke hulda da kasashen yamma.

Idan har mun dauki matakan shisshigin da kasar Amurka ta yi, fakewa da batun “yakar ta’addanci”, a kasashen Larabawa, a matsayin misali. Za mu ga matakan sun shafi yadda aka ta da yake-yake a kasar Iraki, da juyin juya hali a kasar Libya, da yakin basasa a kasar Sham, da dai sauransu. Ko da yake an kaddamar da shisshigi da sunan “adalci”, amma sakamakon da ya haddasa shi ne keta ikon mulkin kai na kasa, da rushewar tsari da oda, da karuwar hare-haren ta’addanci, da rasa rayukan fararen hula, da mawuyacin halin da jama’a ke fuskanta.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

A daura da haka, kuma a nasu bangare, kasashen Larabawa da kasar Sin suna girmama juna, da daukar moriyar junansu da muhimmanci, bisa manufar rashin tsoma baki cikin harkokin gida na sauran kasashe. Misali, kasashen Larabawa na tsayawa kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Yayin da kasar Sin take ta kokarin goyon bayan kasashen Larabawa, a kokarinsu na daidaita maganar Falasdinu, da ta Syria, cikin adalci, da ruwan sanyi.

Bisa tushen girmama juna da musayar ra’ayi cikin daidaito, Sin da kasashen Larabawa suna fahimtar juna da amincewa da juna, inda bangarorin 2 ke kokarin tabbatar da yanayin adalci da zaman lafiya a duniya, gami da neman samun ci gaba na bai daya.

Yanzu haka, ra’ayin “rashin tsoma baki cikin harkokin gida na saura” na kara zama wani abu mai matukar daraja, ganin yadda kasar Amurka ke ci gaba da neman yin babakere a duniya ba tare da jin kunya ba. Kasar na son raba kasashen duniya zuwa rukunoni daban daban masu mabambantan ra’ayoyin siyasa. Kana tana neman ganin bayan tsarin dunkulewar tattalin arizkin duniya waje guda, da yanke alakar hadin gwiwa, don karfafa tsarin da ya fi amfanar kasar Amurka.

Don magance matsaloli sakamakon manufar shissigi da kasar Amurka da kawayenta suke aiwatarwa, dole ne dukkan kasashe masu tasowa, irinsu kasashen Afirka, da kasashen Larabawa, da Sin, su kara yaukaka huldar hadin kai dake tsakaninsu, bisa tushen girmama juna, da samun daidaituwar matsayinsu. Wannan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin ke ta samun karin abokan da suke neman hadin gwiwa da ita, a yankuna daban daban na duniyarmu. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

Next Post

Yunkurin Dakile Kanjamau A 2030 Na Fuskantar Tarnaki A Nijeriya

Related

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

12 hours ago
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
Daga Birnin Sin

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

13 hours ago
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Daga Birnin Sin

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

14 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

15 hours ago
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

16 hours ago
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

18 hours ago
Next Post
Yunkurin Dakile Kanjamau A 2030 Na Fuskantar Tarnaki A Nijeriya

Yunkurin Dakile Kanjamau A 2030 Na Fuskantar Tarnaki A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.