• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsoma Baki Ya Sa Kasar Sin Ke Samun Karin Abokai

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A kwanakin nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping na ziyara a kasar Saudiyya, inda zai halarci taron koli na Sin da kasashen Larabawa, da taron kolin Sin da kwamitin kasashen dake dab da mashigin tekun Pasha ko (GCC). Yadda shugabannin kasashen Larabawa da dama suka taru a gu daya don tattauna harkokin hadin gwiwa tare da kasar Sin ya shaida matsayi mai muhimmanci na kasar Sin a idon kasashen.

Wannan muhimmin matsayi, tushensa shi ne cudanya da cinikin da Sin da kasashen Larabawa suka yi cikin shekaru fiye da 2000 da suka wuce, bi ta hanyar Siliki, da ma karfin tattalin arzikin Sin da ya zama na biyu a duniya, da huldar abota da ta shafi manyan tsare-tsare da kasashen Larabawa suka kulla da kasar Sin.

  • Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce

Haka zalika, a ganina, wani babban dalili na daban da ya sa kasashen Larabawa suke girmama kasar Sin, shi ne manufarta ta “rashin tsoma baki cikin harkokin gida na sauran kasashe”.

Wasu kafofin watsa labaru na kasashen yamma, wadanda ke son shafa wa kasar Sin bakin fenti, su kan bayyana manufar Sin ta rashin tsoma baki a matsayin “rashin daukar nauyi”, ko kuma “rashin niyyar tabbatar da adalci”. Amma hakika Sin na daukar wannan manufa ne da zummar girmama ikon mulki na sauran kasashe, da amincewa da matsayinsu na daya da na kasar Sin. Wannan girmamawa, da zaman daidai wadaida, su ne abubuwan da kasashen Larabawa suka kasa samu, yayin da suke hulda da kasashen yamma.

Idan har mun dauki matakan shisshigin da kasar Amurka ta yi, fakewa da batun “yakar ta’addanci”, a kasashen Larabawa, a matsayin misali. Za mu ga matakan sun shafi yadda aka ta da yake-yake a kasar Iraki, da juyin juya hali a kasar Libya, da yakin basasa a kasar Sham, da dai sauransu. Ko da yake an kaddamar da shisshigi da sunan “adalci”, amma sakamakon da ya haddasa shi ne keta ikon mulkin kai na kasa, da rushewar tsari da oda, da karuwar hare-haren ta’addanci, da rasa rayukan fararen hula, da mawuyacin halin da jama’a ke fuskanta.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

A daura da haka, kuma a nasu bangare, kasashen Larabawa da kasar Sin suna girmama juna, da daukar moriyar junansu da muhimmanci, bisa manufar rashin tsoma baki cikin harkokin gida na sauran kasashe. Misali, kasashen Larabawa na tsayawa kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Yayin da kasar Sin take ta kokarin goyon bayan kasashen Larabawa, a kokarinsu na daidaita maganar Falasdinu, da ta Syria, cikin adalci, da ruwan sanyi.

Bisa tushen girmama juna da musayar ra’ayi cikin daidaito, Sin da kasashen Larabawa suna fahimtar juna da amincewa da juna, inda bangarorin 2 ke kokarin tabbatar da yanayin adalci da zaman lafiya a duniya, gami da neman samun ci gaba na bai daya.

Yanzu haka, ra’ayin “rashin tsoma baki cikin harkokin gida na saura” na kara zama wani abu mai matukar daraja, ganin yadda kasar Amurka ke ci gaba da neman yin babakere a duniya ba tare da jin kunya ba. Kasar na son raba kasashen duniya zuwa rukunoni daban daban masu mabambantan ra’ayoyin siyasa. Kana tana neman ganin bayan tsarin dunkulewar tattalin arizkin duniya waje guda, da yanke alakar hadin gwiwa, don karfafa tsarin da ya fi amfanar kasar Amurka.

Don magance matsaloli sakamakon manufar shissigi da kasar Amurka da kawayenta suke aiwatarwa, dole ne dukkan kasashe masu tasowa, irinsu kasashen Afirka, da kasashen Larabawa, da Sin, su kara yaukaka huldar hadin kai dake tsakaninsu, bisa tushen girmama juna, da samun daidaituwar matsayinsu. Wannan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin ke ta samun karin abokan da suke neman hadin gwiwa da ita, a yankuna daban daban na duniyarmu. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Yunkurin Dakile Kanjamau A 2030 Na Fuskantar Tarnaki A Nijeriya

Yunkurin Dakile Kanjamau A 2030 Na Fuskantar Tarnaki A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.