ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsoma Baki Ya Sa Kasar Sin Ke Samun Karin Abokai

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A kwanakin nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping na ziyara a kasar Saudiyya, inda zai halarci taron koli na Sin da kasashen Larabawa, da taron kolin Sin da kwamitin kasashen dake dab da mashigin tekun Pasha ko (GCC). Yadda shugabannin kasashen Larabawa da dama suka taru a gu daya don tattauna harkokin hadin gwiwa tare da kasar Sin ya shaida matsayi mai muhimmanci na kasar Sin a idon kasashen.

Wannan muhimmin matsayi, tushensa shi ne cudanya da cinikin da Sin da kasashen Larabawa suka yi cikin shekaru fiye da 2000 da suka wuce, bi ta hanyar Siliki, da ma karfin tattalin arzikin Sin da ya zama na biyu a duniya, da huldar abota da ta shafi manyan tsare-tsare da kasashen Larabawa suka kulla da kasar Sin.

  • Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce

Haka zalika, a ganina, wani babban dalili na daban da ya sa kasashen Larabawa suke girmama kasar Sin, shi ne manufarta ta “rashin tsoma baki cikin harkokin gida na sauran kasashe”.

ADVERTISEMENT

Wasu kafofin watsa labaru na kasashen yamma, wadanda ke son shafa wa kasar Sin bakin fenti, su kan bayyana manufar Sin ta rashin tsoma baki a matsayin “rashin daukar nauyi”, ko kuma “rashin niyyar tabbatar da adalci”. Amma hakika Sin na daukar wannan manufa ne da zummar girmama ikon mulki na sauran kasashe, da amincewa da matsayinsu na daya da na kasar Sin. Wannan girmamawa, da zaman daidai wadaida, su ne abubuwan da kasashen Larabawa suka kasa samu, yayin da suke hulda da kasashen yamma.

Idan har mun dauki matakan shisshigin da kasar Amurka ta yi, fakewa da batun “yakar ta’addanci”, a kasashen Larabawa, a matsayin misali. Za mu ga matakan sun shafi yadda aka ta da yake-yake a kasar Iraki, da juyin juya hali a kasar Libya, da yakin basasa a kasar Sham, da dai sauransu. Ko da yake an kaddamar da shisshigi da sunan “adalci”, amma sakamakon da ya haddasa shi ne keta ikon mulkin kai na kasa, da rushewar tsari da oda, da karuwar hare-haren ta’addanci, da rasa rayukan fararen hula, da mawuyacin halin da jama’a ke fuskanta.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

A daura da haka, kuma a nasu bangare, kasashen Larabawa da kasar Sin suna girmama juna, da daukar moriyar junansu da muhimmanci, bisa manufar rashin tsoma baki cikin harkokin gida na sauran kasashe. Misali, kasashen Larabawa na tsayawa kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Yayin da kasar Sin take ta kokarin goyon bayan kasashen Larabawa, a kokarinsu na daidaita maganar Falasdinu, da ta Syria, cikin adalci, da ruwan sanyi.

Bisa tushen girmama juna da musayar ra’ayi cikin daidaito, Sin da kasashen Larabawa suna fahimtar juna da amincewa da juna, inda bangarorin 2 ke kokarin tabbatar da yanayin adalci da zaman lafiya a duniya, gami da neman samun ci gaba na bai daya.

Yanzu haka, ra’ayin “rashin tsoma baki cikin harkokin gida na saura” na kara zama wani abu mai matukar daraja, ganin yadda kasar Amurka ke ci gaba da neman yin babakere a duniya ba tare da jin kunya ba. Kasar na son raba kasashen duniya zuwa rukunoni daban daban masu mabambantan ra’ayoyin siyasa. Kana tana neman ganin bayan tsarin dunkulewar tattalin arizkin duniya waje guda, da yanke alakar hadin gwiwa, don karfafa tsarin da ya fi amfanar kasar Amurka.

Don magance matsaloli sakamakon manufar shissigi da kasar Amurka da kawayenta suke aiwatarwa, dole ne dukkan kasashe masu tasowa, irinsu kasashen Afirka, da kasashen Larabawa, da Sin, su kara yaukaka huldar hadin kai dake tsakaninsu, bisa tushen girmama juna, da samun daidaituwar matsayinsu. Wannan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin ke ta samun karin abokan da suke neman hadin gwiwa da ita, a yankuna daban daban na duniyarmu. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam
Daga Birnin Sin

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa
Daga Birnin Sin

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya
Daga Birnin Sin

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
Next Post
Yunkurin Dakile Kanjamau A 2030 Na Fuskantar Tarnaki A Nijeriya

Yunkurin Dakile Kanjamau A 2030 Na Fuskantar Tarnaki A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.