ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce

by CMG Hausa
4 years ago
Samaniya

Kwanan nan, kumbon Shenzhou-14 dake dauke da ’yan sama jannati uku ya dawo doron duniya. Kafin wannan kuma, ’yan sama jannati na kumbon sun yi musayar aiki tare da takwarorinsu dake cikin kumbon Shenzhou-15, wanda aka harba ba da jimawa ba, daga nan kuma, tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin da ake kira “Tiangong”, ta shiga wani sabon mataki na fara gudanar da harkoki daban daban. Kafin wannan kuma, gwamnatin kasar Sin ta taba sanar da bude tashar ga dukkanin kasashe mambobin MDD.

An ce, tun daga shekarar 2016, kasar Sin ta tattara shirye-shiryen gwaji daga wajen kasashe mambobin MDD wadanda suke so su gudanar a tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, kuma kawo yanzu akwai shirye-shirye 9 na kasashe 17, da suka hada da Switzerland, da Poland, da Jamus, da Italiya, da na wasu rukunoni 23 da aka sanya su cikin jerin shirye-shiryen gwajin kimiyya na farko da za a gudanar a tashar.

  • Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Ya Hade Tashar Binciken Sararin Samaniyar Kasar

Darektar ofishin kula da harkokin sararin samaniya na MDD Simonetta Di Pippo, ta bayyana cewa, yadda kasar Sin ta bude kofar tasharta ta binciken sararin samaniya ya kasance wani muhimmin bangare na shawarar MDD ta “binciken sararin samaniya cikin hadin gwiwa”, kuma misali ne abun yabawa.

ADVERTISEMENT

Sai dai idan an waiwayi baya, Amurka da sauran kasashen yamma sun yi kokarin kafa shingen hana harkokin binciken sararin samaniya da kasar Sin ta gudanar, har ma kasar Amurka ta kafa dokar hana hukumar NASA ta yi hadin gwiwa da kasar Sin, ta hana kasar Sin shiga tashar binciken sararin samaniya ta kasa da kasa. Amma hakan bai hana Sinawa kokarinsu na binciken sararin samaniya ba. Tun bayan da kasar Sin ta fara aiwatar da shirin harba kumbuna masu dauke da mutane a ranar 21 ga watan Satumban shekarar 1992, al’ummar Sinawa sun shafe tsawon shekaru 30 suna kokari bisa karfin kansu, har ma hakarsu ta cimma ruwa.

Ci gaban harkokin binciken sararin samaniya na kasar Sin, ba kawai ya shaida karfin kasar a wannan fanni ba, har ma ya sa kaimin ayyukan binciken sararin samaniya na dan Adam baki daya. Yadda kasa da kasa ke hada gwiwa wajen aiwatar da shirye-shirye a tashar bincike ta kasar Sin, zai taimaka wajen tara fasahohi a wannan fanni, da ma ciyar da harkokin binciken sararin samaniya na dan Adam gaba zuwa wani sabon matsayi.

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin wadda ta bude kofarta ga kasa da kasa, za ta zama gida na ’yan Adam baki daya a sararin samaniya.

Kamar yadda babban mai tsara ayyukan harba kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin, mista Zhou Jianping ya ce, “Aikin da tashar Tiangong ta sanya gaba shi ne, ya zama dakin gwaji na kasar Sin a sararin samaniya, don tallafawa manazarta kimiyya wajen gudanar da nazari da bincike, don amfanin ’yan Adam baki daya.”

A watan Fabarairun bana, hukumar kula da harkokin sararin samaniya na kasar Amurka (NASA) ta sanar da cewa, tashar binciken sararin samaniya ta kasar za ta daina aiki a shekarar 2030, wadda daga baya za ta fado cikin tekun Pasifik. Ta haka, muna iya hasashen cewa, nan da shekaru 8 masu zuwa, tashar Tiangong ta kasar Sin za ta kasance tasha irinta daya kacal ta dan Adam, wadda kuma za ta dauki babban nauyin binciken sararin samaniya. Muna da imanin cewa, tashar za ta hada karfin kasa da kasa, don amfanin dan Adam baki daya, a kokarinta na binciken sararin samaniya. (Lubabatu)

 

Samaniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Next Post
‘Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

'Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.