• Leadership Hausa
Sunday, February 5, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Daga Birnin Sin

Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce

by CMG Hausa
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce

Kwanan nan, kumbon Shenzhou-14 dake dauke da ’yan sama jannati uku ya dawo doron duniya. Kafin wannan kuma, ’yan sama jannati na kumbon sun yi musayar aiki tare da takwarorinsu dake cikin kumbon Shenzhou-15, wanda aka harba ba da jimawa ba, daga nan kuma, tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin da ake kira “Tiangong”, ta shiga wani sabon mataki na fara gudanar da harkoki daban daban. Kafin wannan kuma, gwamnatin kasar Sin ta taba sanar da bude tashar ga dukkanin kasashe mambobin MDD.

An ce, tun daga shekarar 2016, kasar Sin ta tattara shirye-shiryen gwaji daga wajen kasashe mambobin MDD wadanda suke so su gudanar a tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, kuma kawo yanzu akwai shirye-shirye 9 na kasashe 17, da suka hada da Switzerland, da Poland, da Jamus, da Italiya, da na wasu rukunoni 23 da aka sanya su cikin jerin shirye-shiryen gwajin kimiyya na farko da za a gudanar a tashar.

  • Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Ya Hade Tashar Binciken Sararin Samaniyar Kasar

Darektar ofishin kula da harkokin sararin samaniya na MDD Simonetta Di Pippo, ta bayyana cewa, yadda kasar Sin ta bude kofar tasharta ta binciken sararin samaniya ya kasance wani muhimmin bangare na shawarar MDD ta “binciken sararin samaniya cikin hadin gwiwa”, kuma misali ne abun yabawa.

Sai dai idan an waiwayi baya, Amurka da sauran kasashen yamma sun yi kokarin kafa shingen hana harkokin binciken sararin samaniya da kasar Sin ta gudanar, har ma kasar Amurka ta kafa dokar hana hukumar NASA ta yi hadin gwiwa da kasar Sin, ta hana kasar Sin shiga tashar binciken sararin samaniya ta kasa da kasa. Amma hakan bai hana Sinawa kokarinsu na binciken sararin samaniya ba. Tun bayan da kasar Sin ta fara aiwatar da shirin harba kumbuna masu dauke da mutane a ranar 21 ga watan Satumban shekarar 1992, al’ummar Sinawa sun shafe tsawon shekaru 30 suna kokari bisa karfin kansu, har ma hakarsu ta cimma ruwa.

Ci gaban harkokin binciken sararin samaniya na kasar Sin, ba kawai ya shaida karfin kasar a wannan fanni ba, har ma ya sa kaimin ayyukan binciken sararin samaniya na dan Adam baki daya. Yadda kasa da kasa ke hada gwiwa wajen aiwatar da shirye-shirye a tashar bincike ta kasar Sin, zai taimaka wajen tara fasahohi a wannan fanni, da ma ciyar da harkokin binciken sararin samaniya na dan Adam gaba zuwa wani sabon matsayi.

Labarai Masu Nasaba

An Gabatar Da Shirin Tallata Bikin Fitilu Na Gargajiyar Sin A Afrika Ta Kudu Da Habasha

Sin Za Ta Hada Hannu Da MDD Wajen Shawo Kan Kalubalen Duniya

Tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin wadda ta bude kofarta ga kasa da kasa, za ta zama gida na ’yan Adam baki daya a sararin samaniya.

Kamar yadda babban mai tsara ayyukan harba kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin, mista Zhou Jianping ya ce, “Aikin da tashar Tiangong ta sanya gaba shi ne, ya zama dakin gwaji na kasar Sin a sararin samaniya, don tallafawa manazarta kimiyya wajen gudanar da nazari da bincike, don amfanin ’yan Adam baki daya.”

A watan Fabarairun bana, hukumar kula da harkokin sararin samaniya na kasar Amurka (NASA) ta sanar da cewa, tashar binciken sararin samaniya ta kasar za ta daina aiki a shekarar 2030, wadda daga baya za ta fado cikin tekun Pasifik. Ta haka, muna iya hasashen cewa, nan da shekaru 8 masu zuwa, tashar Tiangong ta kasar Sin za ta kasance tasha irinta daya kacal ta dan Adam, wadda kuma za ta dauki babban nauyin binciken sararin samaniya. Muna da imanin cewa, tashar za ta hada karfin kasa da kasa, don amfanin dan Adam baki daya, a kokarinta na binciken sararin samaniya. (Lubabatu)

 

Previous Post

Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

Next Post

‘Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

Related

An Gabatar Da Shirin Tallata Bikin Fitilu Na Gargajiyar Sin A Afrika Ta Kudu Da Habasha
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Shirin Tallata Bikin Fitilu Na Gargajiyar Sin A Afrika Ta Kudu Da Habasha

10 hours ago
Sin Za Ta Hada Hannu Da MDD Wajen Shawo Kan Kalubalen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Hada Hannu Da MDD Wajen Shawo Kan Kalubalen Duniya

11 hours ago
Wang Yi: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Rika Tuntubar Juna Domin Kaucewa Rashin Fahimta
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Rika Tuntubar Juna Domin Kaucewa Rashin Fahimta

12 hours ago
Amurka Ba Ta Cancanci Sukar Kasar Sin Ba
Daga Birnin Sin

Amurka Ba Ta Cancanci Sukar Kasar Sin Ba

23 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Cika Alkawarin Ta Tare Da Yin Abun Da Ya Dace Kan Muhimman Batutuwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Cika Alkawarin Ta Tare Da Yin Abun Da Ya Dace Kan Muhimman Batutuwa

1 day ago
Ya Kamata Amurka Ta Nuna Girmamawa Yayin Sake Bude Ofishin Jakadancinta A Solomon
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Amurka Ta Nuna Girmamawa Yayin Sake Bude Ofishin Jakadancinta A Solomon

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

'Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

February 4, 2023
Gwamnatin Katsina Za Ta Yi Bincike Kan Kisan Da ‘Yan Bindiga Suka Yi Wa Mutum 41

Gwamnatin Katsina Za Ta Yi Bincike Kan Kisan Da ‘Yan Bindiga Suka Yi Wa Mutum 41

February 4, 2023
An Gabatar Da Shirin Tallata Bikin Fitilu Na Gargajiyar Sin A Afrika Ta Kudu Da Habasha

An Gabatar Da Shirin Tallata Bikin Fitilu Na Gargajiyar Sin A Afrika Ta Kudu Da Habasha

February 4, 2023
Kashu

Nijeriya Na Samun Fiye Da Dala Miliyan 250 Daga Kashun Da Ake Fitarwa Waje -Minista

February 4, 2023
Sin Za Ta Hada Hannu Da MDD Wajen Shawo Kan Kalubalen Duniya

Sin Za Ta Hada Hannu Da MDD Wajen Shawo Kan Kalubalen Duniya

February 4, 2023
‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

February 4, 2023
Wang Yi: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Rika Tuntubar Juna Domin Kaucewa Rashin Fahimta

Wang Yi: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Rika Tuntubar Juna Domin Kaucewa Rashin Fahimta

February 4, 2023
Tinubu Yana Kaunar Nijeriya, Ku Zabe Shi – Buhari Ga ‘Yan Nijeriya

Tinubu Yana Kaunar Nijeriya, Ku Zabe Shi – Buhari Ga ‘Yan Nijeriya

February 4, 2023
Rashin Adalci Tsakanin ‘Ya’ya Yana Jawo Fitintinu (Fatawa)

Rashin Adalci Tsakanin ‘Ya’ya Yana Jawo Fitintinu (Fatawa)

February 4, 2023
Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

February 4, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.