ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsoma Baki Ya Sa Kasar Sin Ke Samun Karin Abokai

by CMG Hausa
4 years ago
Kasar Sin

A kwanakin nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping na ziyara a kasar Saudiyya, inda zai halarci taron koli na Sin da kasashen Larabawa, da taron kolin Sin da kwamitin kasashen dake dab da mashigin tekun Pasha ko (GCC). Yadda shugabannin kasashen Larabawa da dama suka taru a gu daya don tattauna harkokin hadin gwiwa tare da kasar Sin ya shaida matsayi mai muhimmanci na kasar Sin a idon kasashen.

Wannan muhimmin matsayi, tushensa shi ne cudanya da cinikin da Sin da kasashen Larabawa suka yi cikin shekaru fiye da 2000 da suka wuce, bi ta hanyar Siliki, da ma karfin tattalin arzikin Sin da ya zama na biyu a duniya, da huldar abota da ta shafi manyan tsare-tsare da kasashen Larabawa suka kulla da kasar Sin.

  • Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce

Haka zalika, a ganina, wani babban dalili na daban da ya sa kasashen Larabawa suke girmama kasar Sin, shi ne manufarta ta “rashin tsoma baki cikin harkokin gida na sauran kasashe”.

ADVERTISEMENT

Wasu kafofin watsa labaru na kasashen yamma, wadanda ke son shafa wa kasar Sin bakin fenti, su kan bayyana manufar Sin ta rashin tsoma baki a matsayin “rashin daukar nauyi”, ko kuma “rashin niyyar tabbatar da adalci”. Amma hakika Sin na daukar wannan manufa ne da zummar girmama ikon mulki na sauran kasashe, da amincewa da matsayinsu na daya da na kasar Sin. Wannan girmamawa, da zaman daidai wadaida, su ne abubuwan da kasashen Larabawa suka kasa samu, yayin da suke hulda da kasashen yamma.

Idan har mun dauki matakan shisshigin da kasar Amurka ta yi, fakewa da batun “yakar ta’addanci”, a kasashen Larabawa, a matsayin misali. Za mu ga matakan sun shafi yadda aka ta da yake-yake a kasar Iraki, da juyin juya hali a kasar Libya, da yakin basasa a kasar Sham, da dai sauransu. Ko da yake an kaddamar da shisshigi da sunan “adalci”, amma sakamakon da ya haddasa shi ne keta ikon mulkin kai na kasa, da rushewar tsari da oda, da karuwar hare-haren ta’addanci, da rasa rayukan fararen hula, da mawuyacin halin da jama’a ke fuskanta.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A daura da haka, kuma a nasu bangare, kasashen Larabawa da kasar Sin suna girmama juna, da daukar moriyar junansu da muhimmanci, bisa manufar rashin tsoma baki cikin harkokin gida na sauran kasashe. Misali, kasashen Larabawa na tsayawa kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Yayin da kasar Sin take ta kokarin goyon bayan kasashen Larabawa, a kokarinsu na daidaita maganar Falasdinu, da ta Syria, cikin adalci, da ruwan sanyi.

Bisa tushen girmama juna da musayar ra’ayi cikin daidaito, Sin da kasashen Larabawa suna fahimtar juna da amincewa da juna, inda bangarorin 2 ke kokarin tabbatar da yanayin adalci da zaman lafiya a duniya, gami da neman samun ci gaba na bai daya.

Yanzu haka, ra’ayin “rashin tsoma baki cikin harkokin gida na saura” na kara zama wani abu mai matukar daraja, ganin yadda kasar Amurka ke ci gaba da neman yin babakere a duniya ba tare da jin kunya ba. Kasar na son raba kasashen duniya zuwa rukunoni daban daban masu mabambantan ra’ayoyin siyasa. Kana tana neman ganin bayan tsarin dunkulewar tattalin arizkin duniya waje guda, da yanke alakar hadin gwiwa, don karfafa tsarin da ya fi amfanar kasar Amurka.

Don magance matsaloli sakamakon manufar shissigi da kasar Amurka da kawayenta suke aiwatarwa, dole ne dukkan kasashe masu tasowa, irinsu kasashen Afirka, da kasashen Larabawa, da Sin, su kara yaukaka huldar hadin kai dake tsakaninsu, bisa tushen girmama juna, da samun daidaituwar matsayinsu. Wannan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin ke ta samun karin abokan da suke neman hadin gwiwa da ita, a yankuna daban daban na duniyarmu. (Bello Wang)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Yunkurin Dakile Kanjamau A 2030 Na Fuskantar Tarnaki A Nijeriya

Yunkurin Dakile Kanjamau A 2030 Na Fuskantar Tarnaki A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.