• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Wadatar Kayan Aiki: Yadda Nijeriya Ta Kasa Dakatar Da Asarar Naira Tiriliyan 1.4 A Sashen Kiwon Lafiya

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Aiki

Gwamnatin tarayya ta gaza cika alkawuran da ta dauka na aiwatar da tsare-tsaren da za su kai ga farfado da bangaren kiwon lafiya, lamarin da ke bude wagegen hanyar kashe makudan kudade a bangarorin kiwon lafiya, kama daga gine-ginen asibitoci, kayan aiki, maguna, wanda ya janyo rashin samun kiwon lafiya mai inganci.

Dukkanin gwamnatocin baya da na yanzu sun himmatu wajen samar da kiwon lafiya cikin rahusa da sauki ga jama’a, amma alkarin har yanzu bai samu cimmawuwa ba.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • Alhajin Jihar Jigawa Ya Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta Ga Mai Shi A Makka

LEADERSHIP ta labarto cewa gwamnatin tarayya ta sanya kiwon lafiya cikin muhimman bangarorin da take bai wa fifiko, amma tsawon shekaru babu wani abun a zo a gani da ta iya tabuka a bangaren.

A cewar gwamnatin, daga cikin manufarta na ganin an samar da kiwon lafiya mai inganci cikin rahusa, shi ne kawo mafita ga matsalolin kiwon lafiya, rungumar sabbin hanyoyin fasa, da kuma rage yawan kashe kudaden neman jinya zuwa kasashen ketare.

Sai dai har yanzu tsarin kiwon lafiya a asibitocin gwamnati da na masu zaman kansu na fama da matsaloli ciki har da na rashin ci gaba da rashin wadatar kayan aiki. Asibitocin gwamnati ma sun fi fama da matsalar rashin kyawun kayan abinci, gine-ginen da suka dace, rashin maguna da karancin kwararru da kuma karancin kudaden gudanarwa.

LABARAI MASU NASABA

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

Masu lura da lamuran sun ce wadannan matsalolin sun kasance dalilin da ke janyo rashin samun kiwon lafiya a kan lokaci.

Yankunan karkara na kan gaba wajen fama da rashin asibitoci da samun kiwon lafiya idan aka kwatanta da birane. Asibitoci masu zaman kansu ma sun fi na gwamnatoci wadatar kayan aiki, lamarin da ke sanya jama’a kashe makuden kudade wajen neman jinya a asibitocin kudi.

A cewar BPE, dala biliyan (Tiriliyan 1.4) ne ake rasawa duk shekara wajen jinya ga dubban ‘yan Nijeriya da ke zuwa kasashen waje domin neman kiwon lafiya mai inganci da nagarta.

Bangaren kiwon lafiya a Nijeriya na fuskantar gibin kudade, wanda aka kiyasce cewa biliyoyin daloli ne ke salwanta a duk shekara.

Hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta ba da shawarar a kara ware kaso 15 na kasafin kudin kowace kasa ga sashin kiwon lafiya, sai dai kasafin Nijeriya na gaza cika wannan shawarar. A shekarun baya, Nijeriya tana ware kaso 4-5 ne duk shekara ga bangaren kiwon lafiya, lamarin da ke barin wagegen gibi na kudade.

Sashin kiwon lafiya a jihohi na cikin halin ha-ula’i, asibitoci da dama ba su da wadatar kayan aiki da na kwararru. A wasu asibitoci da dama, hatta wutar lantarki, ruwa da sauran muhimman abubuwa ba su samu balle a yi maganar ingancinsu, lamarin da ke janyo babban matsala wajen samar da kiwon lafiya mai nagarta.

Bugu da kari, akwai matsalar ma’aikatan kiwon lafiya, daktoci, nas-nas, kwararru, inda wasu suka zabi su tafi kasashen waje domin yin aiki a maimakon yi a Nijeriya sakamakon matsalolin da bangaren kiwon lafiya ke fuskanta ciki har da rashin biyan kudin da ya dace da sauransu.

Lamarin na kara janyo karancin ma’aikatan kiwon lafiya da ke janyo yawan mace-mace, karancin samun aminci da asibitocin gwamnati.

Nijeriya kasa ce da take kan gaba wajen yawaitar mace-macen yara jarirai da mata masu juna biyu, yawan kamuwa da cutuka da suka hada da maleriya, tarin fuka, cuta mai karya garkuwar jiki, cutar suka, yawan jini da sauran cutuka masu hatsari, kuma asibitoci na fuskantar manyan kalubale.

Wata daktar da ta nemi a sakaye sunanta da ke aiki da gwamnatin tarayya ta ce, “Rashin wadatar kudade na daga cikin manyan matsalolin da sashin kiwon lafiya ke fuskanta, wanda hakan ke janyo karancin ba da kiwon lafiya da samun sakamako mai inganci,” ta shaida.

A bisa rashin wadatar kayan aiki da kwararru a kasar nan, ‘yan Nijeriya da dama sukan yanke shawarar fita kasashen waje domin neman lafiya, lamarin da ake asarar makuden kudade, domin fita jinyar na lakume musu miliyoyin naira ga kowani majinyaci.

A kiyasin da aka yi, ‘yan Nijeriya na kashe dala biliyan 1.2 a kowace shekara wajen yawon neman lafiya a kasashen waje, domin neman jinya mai inganci a kasashe irin su India, Amurka, Ingila da sauransu.

Ma’aikatan kiwon lafiya da dama sun ce domin shawo kan gibin da ake da shi a bangaren kiwon lafiyan jihohi da na tarayya, akwai bukatar sake fasalin tsarin kiwon lafiya da ake tafiya a kai da kuma zuba makuden kudade a fannin.

Wani likita a Abuja, Dakta Idris Hameed, ya shaida cewa, “Akwai bukatar gwamnati ta kara kasafin kudin da take ware wa sashin kiwon lafiya, da tabbatar da cewa kudaden da aka ware an yi amfani da su bisa gaskiya kuma yadda ya dace.

“Bugu da kari, hadin kai da masu zaman kansu na da matukar muhimmanci ta yadda za a samu shawo kan gibin da ake da shi wajen samar da kiwon lafiya mai inganci.

“Akwai bukatar a kara horas da ma’aikatan kiwon lafiya, da daukan sabbi, ba da yanayin aiki mai inganci. Shawo kan irin wadannan matsalolin na bukatar hadin gwiwar kowa da kowa daga bangaren masu ruwa da tsai, ciki har da gwamnatici, masu zaman kansu na kasashen waje domin tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya na samun wadataccen kiwon lafiya kuma mai inganci,” ya shaida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Manyan Labarai

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci
Labarai

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano
Manyan Labarai

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Next Post
NAHCON Ta Gargadi Alhazai Su Guji Tsarabar Ruwan Zamzam 

NAHCON Ta Gargadi Alhazai Su Guji Tsarabar Ruwan Zamzam 

LABARAI MASU NASABA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.