• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Wutar Lantarki A Arewa Zai Dauki Tsawon Lokacin Kafin Ya Gyaru – Rahoto

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Discos
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yunkurin warware matsalar wutar lantarki a Arewacin Nijeriya na kara yin kamari, yayin da wasu sabbin bayanai suka sake bayyana dangane da aikata almundahana da kuma rashin kulawa da ya yi sanadiyar jefa yankin duhu na tsawon lokaci.

 

Rahotanni na baya-bayan nan sun nuna cewa, akwai karancin kayan aikin samar da wutar lantarkin a yankunan Arewa Maso Gabas da kuma Arewa Maso Yamma.

  • A Karon Farko Adadin Motoci Masu Aiki Da Sabon Makamashi Da Kasar Sin Ke Kerawa Duk Shekara Ya Zarce Miliyan 10
  • Ya Kamata Rungumar Hadin Gwiwa Da Yin Komai A Bude Su Zamo Ginshikan Ci Gaban Yankin Asiya Da Pacifik A Nan Gaba

Wani bincike ya bayyana cewa, shirin gyara tare da fadada harkar samar da wutar lantarkin; wanda aka tsara don samun sassaucin matsalar, ya lalace ne sakamakon yin sama da fadi da dala biliyan 1.66.

 

Labarai Masu Nasaba

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Bugu da kari, sama da dala biliyan 500 da aka ware na takwaransa; wanda ya hada da muhimman layukan da suka hada da Sakkwato, Kaura Namoda, Katsina, Jogana, Dutse, Azare, Fataskum, Damaturu, Yola, Jalingo, Mambila, Kashimbilla, Ogoja, Ikom, da kuma Kalaba; shi ma ba a san inda kudaden suka yi ba.

 

Haka zalika, yankin Arewa Maso Gabas; ya dogara ne da layin samar da wutar na Jos zuwa Gwambe, mai karfin kb330; wanda hakan ya bar yankunan biyu cikin mawuyacin hali na rashin wannan wuta.

 

Wani abin sha’awa shi ne, yayin da aka kammala aikin layin Jos zuwa Kaduna mai karfin kb330 a baya; har yanzu ba a gama kammala hanyoyin da ake bukata a Jos da Kaduna ba. Domin kuwa, an soke kwangilolin wadannan muhimman abubuwa tare da mayar da su ga Injiniyoyin Kamfanin tattara wutar lantarki da kuma rarraba ta (TCN), wadanda ke da sassan da aka kwashe daga Anambra.

 

“Da a ce an bar Injiniyoyin TCN sun ci gaba da aikin, da za a iya samun wutar har tsawon wata biyar. Amma duk da haka, sai aka mayar da kwangilar zuwa ga ‘yan kwangilar da suka kammala ayyukan da suka gabata,” in ji majiyoyi.

 

Yayin da matsalar wutar lantarkin ta ci gaba da yin kamari, ba a dauki wani matakin yin binciken gaggawa ba, duk kuwa da cewa al’ummar Arewa; sun cancanci a ba su kulawa ta musamman tare da daukan kwararan matakai, don dawo da wutar lantarki a yankin, a cewar rahoton.

 

A gefe guda kuma, Hukumar EFCC ta ce; za ta binciki kamfanonin wutar lantarki, domin bankado sirrin da ke tattare da lalacewar wutar lantarkin.

 

Shugaban Hukumar EFCC, Ola Olukayode ne ya bayyana hakan a Abuja ranar Talatar da ta wuce, yayin da kwamitin majalisar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa; ya ziyarci hedikwatar Hukumar ta EFCC, domin gudanar da aikin sa ido.

 

Shugaban na EFCC ya ce, daya daga cikin matsalolin da kasar nan ta fuskanta daga shekara 15 zuwa 20 da suka gabata, shi ne yadda ayyukan kasafin kudi ke kasa da kashi 20 cikin 100 na ayyukan da ake aiwatarwa. Wasu kamfanonin samar da wutar lantarki na sayen kayayyaki marasa inganci, wadanda ke haddasa lalacewar wutar akai-akai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Binciken CGTN Ya Nuna Amincewa Da Kokarin Kasar Sin Dangane Da Aiwatar Da Matakan Dakile Sauyin Yanayi

Next Post

Katsewar Lantarki: Masu Masana’antu Sun Kashe Naira Biliyan 238.3 Wajen Samun Wuta

Related

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
Manyan Labarai

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

48 minutes ago
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
Labarai

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

8 hours ago
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata
Labarai

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

9 hours ago
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
Labarai

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

10 hours ago
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal
Labarai

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

11 hours ago
Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 
Labarai

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

12 hours ago
Next Post
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko

Katsewar Lantarki: Masu Masana’antu Sun Kashe Naira Biliyan 238.3 Wajen Samun Wuta

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

August 15, 2025
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

August 14, 2025
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

August 14, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

August 14, 2025
Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

August 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Kama Mutane 107 Da Ake Zargi, Sun Ceto Mutane 20 A Cikin Mako Guda – DHQ

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.