• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Wutar Lantarki A Arewa Zai Dauki Tsawon Lokacin Kafin Ya Gyaru – Rahoto

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Discos
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yunkurin warware matsalar wutar lantarki a Arewacin Nijeriya na kara yin kamari, yayin da wasu sabbin bayanai suka sake bayyana dangane da aikata almundahana da kuma rashin kulawa da ya yi sanadiyar jefa yankin duhu na tsawon lokaci.

 

Rahotanni na baya-bayan nan sun nuna cewa, akwai karancin kayan aikin samar da wutar lantarkin a yankunan Arewa Maso Gabas da kuma Arewa Maso Yamma.

  • A Karon Farko Adadin Motoci Masu Aiki Da Sabon Makamashi Da Kasar Sin Ke Kerawa Duk Shekara Ya Zarce Miliyan 10
  • Ya Kamata Rungumar Hadin Gwiwa Da Yin Komai A Bude Su Zamo Ginshikan Ci Gaban Yankin Asiya Da Pacifik A Nan Gaba

Wani bincike ya bayyana cewa, shirin gyara tare da fadada harkar samar da wutar lantarkin; wanda aka tsara don samun sassaucin matsalar, ya lalace ne sakamakon yin sama da fadi da dala biliyan 1.66.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Bugu da kari, sama da dala biliyan 500 da aka ware na takwaransa; wanda ya hada da muhimman layukan da suka hada da Sakkwato, Kaura Namoda, Katsina, Jogana, Dutse, Azare, Fataskum, Damaturu, Yola, Jalingo, Mambila, Kashimbilla, Ogoja, Ikom, da kuma Kalaba; shi ma ba a san inda kudaden suka yi ba.

 

Haka zalika, yankin Arewa Maso Gabas; ya dogara ne da layin samar da wutar na Jos zuwa Gwambe, mai karfin kb330; wanda hakan ya bar yankunan biyu cikin mawuyacin hali na rashin wannan wuta.

 

Wani abin sha’awa shi ne, yayin da aka kammala aikin layin Jos zuwa Kaduna mai karfin kb330 a baya; har yanzu ba a gama kammala hanyoyin da ake bukata a Jos da Kaduna ba. Domin kuwa, an soke kwangilolin wadannan muhimman abubuwa tare da mayar da su ga Injiniyoyin Kamfanin tattara wutar lantarki da kuma rarraba ta (TCN), wadanda ke da sassan da aka kwashe daga Anambra.

 

“Da a ce an bar Injiniyoyin TCN sun ci gaba da aikin, da za a iya samun wutar har tsawon wata biyar. Amma duk da haka, sai aka mayar da kwangilar zuwa ga ‘yan kwangilar da suka kammala ayyukan da suka gabata,” in ji majiyoyi.

 

Yayin da matsalar wutar lantarkin ta ci gaba da yin kamari, ba a dauki wani matakin yin binciken gaggawa ba, duk kuwa da cewa al’ummar Arewa; sun cancanci a ba su kulawa ta musamman tare da daukan kwararan matakai, don dawo da wutar lantarki a yankin, a cewar rahoton.

 

A gefe guda kuma, Hukumar EFCC ta ce; za ta binciki kamfanonin wutar lantarki, domin bankado sirrin da ke tattare da lalacewar wutar lantarkin.

 

Shugaban Hukumar EFCC, Ola Olukayode ne ya bayyana hakan a Abuja ranar Talatar da ta wuce, yayin da kwamitin majalisar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa; ya ziyarci hedikwatar Hukumar ta EFCC, domin gudanar da aikin sa ido.

 

Shugaban na EFCC ya ce, daya daga cikin matsalolin da kasar nan ta fuskanta daga shekara 15 zuwa 20 da suka gabata, shi ne yadda ayyukan kasafin kudi ke kasa da kashi 20 cikin 100 na ayyukan da ake aiwatarwa. Wasu kamfanonin samar da wutar lantarki na sayen kayayyaki marasa inganci, wadanda ke haddasa lalacewar wutar akai-akai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Binciken CGTN Ya Nuna Amincewa Da Kokarin Kasar Sin Dangane Da Aiwatar Da Matakan Dakile Sauyin Yanayi

Next Post

Katsewar Lantarki: Masu Masana’antu Sun Kashe Naira Biliyan 238.3 Wajen Samun Wuta

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

4 hours ago
Lantarki
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

5 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

6 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

9 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

12 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

12 hours ago
Next Post
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko

Katsewar Lantarki: Masu Masana’antu Sun Kashe Naira Biliyan 238.3 Wajen Samun Wuta

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Lantarki

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.