• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Kakakin Majalisar wakilai ta tarayya, Rt. Hon. Yakubu Dogara ya aike da wasikar korafi wa Sufeto Janar na ‘yansandan Nijeriya, IGP Usman Baba Alkali dangane da zargin yunkurin kasheshi da wani dan mazabarsa ke yi.

Tsohon Kakakin ya bayyana sunansa wanda ke kokarin kashe sa din da cewa shine Barau Joel Amos wanda a cewarsa balo-balo ya yi ikirarin zai sayi bindiga tare da kashe shi da wasu ‘yan mazabarsa su uku masu suna Barr. Istifanus Bala Gambar, Rabaran Markus Musa (Shugaban kungiyar Kiristoci na Tafawa Balewa) da Mr. Emmanuel (Shugaban NL, na T/Balewa).

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 69 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Bauchi

Yakubu Dogara ya shaida wa IGP Alkali cewa akwai zargin hada kai da wasu jami’an ‘yansanda masu suna Insifekta Dakat Samuel da Insifekta Auwalu Mohammed da shi Barau Joel Amos (Sarkin Yaki) wajen shirya wannan makarkashiyar tare da sayen bindigogi a hannunsu domin kashe shi.

Dogara ya shaida wa shugaban ‘yansandan cewa tunin kes din yake gaban DCP na sashin binciken na manyan laifuka ta rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, amma bisa girman lamarin ya ga dacewar sanar da shi domin fadada bincike, “Batu ne da ya shafi sace makamanku daga wasu jami’an da aka daura wa alhakin kula da makamai a wurin adanasu, shi Barau Joel Amos ko zai saya ko yana ma yana sayen bindigogi daga wajen jami’an.”

Dogara ya kara da cewa abun mamakin shine babu wani shawara a hukumance da ‘yansanda suka fitar dangane da wannan mummunar barazanar da ake yi wa rayuwarsu duk kuwa da cewa ana samun kesa-kesan garkuwa da mutane da kashe wasu ma musamman a gundumar Lere da ke karamar hukumar Tafawa Balewa a jihar Bauchi.

Labarai Masu Nasaba

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Dogaran sai ya buga misali da harin baya-bayan nan da wasu ‘yan bindiga suka kai kauyen Boto da ke gundumar Lere inda suka yi garkuwa da ‘yan uwan tsohon gwamnan Jihar Bauchi, Ahmadu Adamu Mu’azu da kashe wani, kan hakan ya nuna cewa akwai bukatar daukan matakan kan lamarin.

Ya ce irin wannan lamarin abun ne da ke bukatar gaggauta daukar matakin tare da cafke Barau Joel Amos domin zufafa bincike.

Hon. Yakubu Dogara ya kuma ce akwai matukar bukatar a binciki Barau Amos kan matsalolin tsaro da suke faruwa a yankin tare da bincikar inda yake samun kudaden sayen makamai tare da bibiyar bayanan shigar kudi da fitar kudi na asusun ajiyarsa hadi da binciken wayarsa.

Ya ce akwai bayanan da suke da su da dama da ke nuna cewa shi Barau Joel Amos na da hannu a zarge-zarge da dama don haka akwai bukatar a tsare shi tare da zurfafa bincike a kansa.

Ya yi fatan cewa Shugaban na ‘yansanda ba zai yi wasa da wannan batun ba inda zai kaddamar da bincike domin tabbatar da inganci tsaro da kare rayuka da dukiyar jama’an yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Afirka Zata Iya Lashe Kofin Duniya A Qatar – Samuel Eto’o 

Next Post

Ga Yadda Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Related

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

6 hours ago
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina
Labarai

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

2 days ago
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC
Siyasa

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

3 days ago
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12
Siyasa

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

3 days ago
Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa
Siyasa

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

4 days ago
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
Siyasa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

4 days ago
Next Post
Ga Yadda Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Ga Yadda Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

August 5, 2025
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

August 5, 2025
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

August 5, 2025
Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.