• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribadu Ya Bukaci NLC Ta Janye Yajin Aiki, Ya Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Ajaero

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ribadu Ya Bukaci NLC Ta Janye Yajin Aiki, Ya Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Ajaero
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya bukaci kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC da ta janye yajin aikin da ta fara.

Kazalika, Ribadu ya yi Allah wadai da cin zarafin da aka yi wa shugaban NLC, Kwamared Joe Ajaero ranar 1 ga watan Nuwamba, 2023 a Owerri, babban birnin Jihar Imo.

  • Matar Aure Ta Kone Gidan Mijinta Saboda Ya Ki Sakin Ta
  • Napoli Ta Kori Rudi Garcia Wata 4 Bayan Nada Shi A Matsayin Koci

A cikin wata sanarwa da shugaban sashen sadarwa na ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Zakari Mijinyawa ya fitar, ya ce an kama wadanda ake zargi da dukan Ajaero .

Sanarwar ta kara da cewa ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, ya damu da shiga yajin aikin da shugabannin kungiyoyin kwadagon karkashin jagorancin NLC da TUC suka soma a fadin kasar nan.

“Hukumar NSA ta damu matuka game da illar da yajin aikin zai yi ga rayuwar talakawan Nijeriya da kuma tattalin arziki da sauran manyan muradun kasa.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

“Kamar yadda shugabannin NLC suka shaida, nan take NSA ta shiga tsakani domin samun labarin halin da Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), Kwamared Joseph Ajero ya yi a Owerri, Jihar Imo.

“Hukumar NSA ta yi nadamar faruwar abin da ya faru da Ajaero kuma ta yi Allah wadai da lamarin gaba daya saboda ya saba wa doka da ‘yancin fadin albarkacin baki da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da gwamnatinsa ke bi.”

Sanarwar ta kara da cewa gwamnatin tarayya ba za ta lamunci irin wannan cin zarafi ga kowane dan kasa ba .

“Sakamakon faruwar lamarin an umarci hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da gurfanar da wadanda suka aikata laifin.

“Bayanin da aka samu na nuni da cewa an riga an kama wasu da ke da hannu a lamarin. Za a bayyana sakamakon binciken da zarar an kammala bincike,” in ji shi.

Don haka gwamnatin tarayya ta yi kira ga shugabannin kwadago da su janye yajin aikin da suke yi a halin yanzu, domin bayar da damar tattaunawa cikin ruwan sanyi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AjaeroNlcNSARibaduTUCYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matar Aure Ta Kone Gidan Mijinta Saboda Ya Ki Sakin Ta

Next Post

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Ya Bar Saudiyya Zuwa Guinea Bissau

Related

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

5 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

6 hours ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

8 hours ago
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

11 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

13 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

21 hours ago
Next Post
Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Ya Bar Saudiyya Zuwa Guinea Bissau

Ranar 'Yancin Kai: Tinubu Ya Bar Saudiyya Zuwa Guinea Bissau

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.