ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribadu Ya Bukaci NLC Ta Janye Yajin Aiki, Ya Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Ajaero

by Sadiq
3 years ago
Ribadu

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya bukaci kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC da ta janye yajin aikin da ta fara.

Kazalika, Ribadu ya yi Allah wadai da cin zarafin da aka yi wa shugaban NLC, Kwamared Joe Ajaero ranar 1 ga watan Nuwamba, 2023 a Owerri, babban birnin Jihar Imo.

  • Matar Aure Ta Kone Gidan Mijinta Saboda Ya Ki Sakin Ta
  • Napoli Ta Kori Rudi Garcia Wata 4 Bayan Nada Shi A Matsayin Koci

A cikin wata sanarwa da shugaban sashen sadarwa na ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Zakari Mijinyawa ya fitar, ya ce an kama wadanda ake zargi da dukan Ajaero .

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, ya damu da shiga yajin aikin da shugabannin kungiyoyin kwadagon karkashin jagorancin NLC da TUC suka soma a fadin kasar nan.

“Hukumar NSA ta damu matuka game da illar da yajin aikin zai yi ga rayuwar talakawan Nijeriya da kuma tattalin arziki da sauran manyan muradun kasa.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

“Kamar yadda shugabannin NLC suka shaida, nan take NSA ta shiga tsakani domin samun labarin halin da Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), Kwamared Joseph Ajero ya yi a Owerri, Jihar Imo.

“Hukumar NSA ta yi nadamar faruwar abin da ya faru da Ajaero kuma ta yi Allah wadai da lamarin gaba daya saboda ya saba wa doka da ‘yancin fadin albarkacin baki da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da gwamnatinsa ke bi.”

Sanarwar ta kara da cewa gwamnatin tarayya ba za ta lamunci irin wannan cin zarafi ga kowane dan kasa ba .

“Sakamakon faruwar lamarin an umarci hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da gurfanar da wadanda suka aikata laifin.

“Bayanin da aka samu na nuni da cewa an riga an kama wasu da ke da hannu a lamarin. Za a bayyana sakamakon binciken da zarar an kammala bincike,” in ji shi.

Don haka gwamnatin tarayya ta yi kira ga shugabannin kwadago da su janye yajin aikin da suke yi a halin yanzu, domin bayar da damar tattaunawa cikin ruwan sanyi.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Ya Bar Saudiyya Zuwa Guinea Bissau

Ranar 'Yancin Kai: Tinubu Ya Bar Saudiyya Zuwa Guinea Bissau

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.