ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribadu Ya Bukaci NLC Ta Janye Yajin Aiki, Ya Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Ajaero

by Sadiq
3 years ago
Ribadu

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya bukaci kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC da ta janye yajin aikin da ta fara.

Kazalika, Ribadu ya yi Allah wadai da cin zarafin da aka yi wa shugaban NLC, Kwamared Joe Ajaero ranar 1 ga watan Nuwamba, 2023 a Owerri, babban birnin Jihar Imo.

  • Matar Aure Ta Kone Gidan Mijinta Saboda Ya Ki Sakin Ta
  • Napoli Ta Kori Rudi Garcia Wata 4 Bayan Nada Shi A Matsayin Koci

A cikin wata sanarwa da shugaban sashen sadarwa na ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Zakari Mijinyawa ya fitar, ya ce an kama wadanda ake zargi da dukan Ajaero .

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, ya damu da shiga yajin aikin da shugabannin kungiyoyin kwadagon karkashin jagorancin NLC da TUC suka soma a fadin kasar nan.

“Hukumar NSA ta damu matuka game da illar da yajin aikin zai yi ga rayuwar talakawan Nijeriya da kuma tattalin arziki da sauran manyan muradun kasa.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

“Kamar yadda shugabannin NLC suka shaida, nan take NSA ta shiga tsakani domin samun labarin halin da Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), Kwamared Joseph Ajero ya yi a Owerri, Jihar Imo.

“Hukumar NSA ta yi nadamar faruwar abin da ya faru da Ajaero kuma ta yi Allah wadai da lamarin gaba daya saboda ya saba wa doka da ‘yancin fadin albarkacin baki da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da gwamnatinsa ke bi.”

Sanarwar ta kara da cewa gwamnatin tarayya ba za ta lamunci irin wannan cin zarafi ga kowane dan kasa ba .

“Sakamakon faruwar lamarin an umarci hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da gurfanar da wadanda suka aikata laifin.

“Bayanin da aka samu na nuni da cewa an riga an kama wasu da ke da hannu a lamarin. Za a bayyana sakamakon binciken da zarar an kammala bincike,” in ji shi.

Don haka gwamnatin tarayya ta yi kira ga shugabannin kwadago da su janye yajin aikin da suke yi a halin yanzu, domin bayar da damar tattaunawa cikin ruwan sanyi.

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
Manyan Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
Manyan Labarai

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Next Post
Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Ya Bar Saudiyya Zuwa Guinea Bissau

Ranar 'Yancin Kai: Tinubu Ya Bar Saudiyya Zuwa Guinea Bissau

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.