• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rike Iyayen Gida Masu Amana Na Daga Sirrin Samun Nasara A Kannyywood – Muhammadu Murtala

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
in Nishadi
0
Rike Iyayen Gida Masu Amana Na Daga Sirrin Samun Nasara A Kannyywood – Muhammadu Murtala
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin fitattun Jaruman fina-finan Hausa cikin masana’antar Kannywood, kuma Jarumi mai taka rawa a cikin shirin Dadin Kowa na Arewa24, wanda ya shafe shekaru sha biyar a cikin masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, MUHAMMADU MURTALA wanda aka fi sani da DANTANI MAI SHAYI. Ya warware zare da abawa game da abubuwan da masana’antar ke bukata a wajen duk wani me shirin zama jarumi. Bugu da kari jarumin ya yi kira ga gwamnati game da irin matsalolin da masana’antar ke fuskanta tare da hanyar magance su. Dadin dadawa jarumin ya bayyana irin kalubalen da ya fuskanta yayin shiga cikin masana’antar, har ma da wasu batutuwan masu yawa wadanda suka shafi rayuwarsa. Ga dai tattaunawar tare da RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

Da farko za ka fadawa masu karatu cikakken sunanka tare da dan takaitaccen tarihinka?
Sunana Muhammadu Murtala wanda aka fi sani da Dan Tani Mai Shayi a Dadin Kowa. An haife ni a unguwar ‘Brigade’ Kabarin Rakka, na yi firamare a ‘Kawo Unguwar Gaya Special Primary School’ da ke Unguwar Gaya. Daga nan na tafi ‘Secondary School Stadium’, daga nan kuma na je KAS. Ina da mata guda daya da yarinya daya.

Me ya ja hankalinka har ka tsunduma cikin masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood?
Abin da ya ja hankalina har na shigo cikin masana’antar shi ne, Tun a makarantar Sakandare irin dirama irin wadda ake yi a makaranta, shi ya ja hankalina. Daga nan sai muka kafa kungiya ta dirama mai suna ‘Kainuwa’, mun kafa ta a Badawa, daga nan kuma sai muka yi wata kungiyar a Dakata, sai kuma muka yi Le Jan Zaki, daga nan sai na dawo nake Sakatare na Ali Jita, tun lokacin muke tare da Ali Jita har kawo iyanzu. Bayan nan kuma na tafi Arewa24 muke Dadin Kowa, amma ban da Dadin Kowa na yi fina-finai da yawa, kamar su; Sabuwar Sangaya, Sarkin Barayi, da dai sauransu suna da yawa.

Za ka yi kamar shekara nawa da fara fim?
Zan kai kamar shekara goma sha biyar

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance?
Gaskiya akwai gwagwarmaya sosai, ka tashi ka shiga nan, kai ne can. Ita harkar industiri daman farko kar ka sa ran sai ka samu kudi a cikinta, farko ka fara da neman suna shi ne farko, kuma sai ka zamto mai ladabi da biyayya, sai ka zamto mutum ne me sirri, sai ka zamto mutum ne mara rainuwa, sai ka zamto mutum ne mara daukar magana ka kai nan – ka kai can. To indai kana haka to za ka ci gaba kuma ka zamto mai addu’a, kuma ka rike iyayen gida masu amana, wannan ita ce kadan daga cikin gwagwarmayar Industiri, ka ji – ka ki ji, ka gani – ka ki gani, haka harkar take.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Muhammadu Murtala

Lokacin da ka fara sanarwa iyayenka cewar kana sha’awar shiga cikin masana’antar, shin ka fuskanci wani kalubale daga gare su ko kuwa?
Eh! Gaskiya lokacin dana gama makaranta ina dan aiki haka sai in daina, idan aka sama mun aiki sai in daina na rinka tafiya wajen harkar dirama, tun muna irin ta gidan suna da gidan biki, daga karshe dai mahaifina da bakinsa yake cewa da sauran ‘yan uwana “Tunda ga shi ana ta sama masa aiki amma ya ki tsayawa, hankalinsa ya fi karkata a kan wasan Hausa to a yi masa addu’a Allah ya sa abincinsa a nan yake, Allah sa kuma ya gama lafiya, kuma Allah ya daukaka shi a sana’ar”. Kin ga wannan addu’ar ta mahaifa ita muke cin gajiyarta. Ni babu wani kalubale dana samu daya wuce wannan, sun fahimce ni kuma sun san ya dansu yake, tun daga nan kuma duk inda na je nake samun nasara.

Duk abin da aka ce bakonsa ne kai a lokacin shi ne farko, dole ka ji wani iri, don a lokacin ji na yi kamar kafata ma ba za ta dauke ni ba, kamar ina karkarwa, kafata tana karkarwa, in kalli nan a ce ga yadda za ka yi, da haka – da haka har na yi.

Da wanne fim ka fara?
Fim din dana fara shi ne; Wasiyya, da Dan Adam Butulu. A Wasiyya na tawo ina gudu har Jarumin ya girma, Dan Adam Butulu kuma fitowa daya nayi, na fito a mai gadi, daga nan sai muka zo muka yi Bakandamiya na Ali Jita, da Murmushin Alkawari, su Babban Zaure, Mutum da Addininsa, da dai sauran fina-finai, dan yanzu haka ma akwai wani Siris fim da zai fita na Ali Jita mai suna Aliya shi ma na taka rawa sosai a cikin fim din.

Ko za ka iya tuna yawan adadin fina-finan da ka yi?
A takaice dai za su yi kamar guda Talatin ko Arba’in, ba zan iya kirgawa daidai ba, sabida suna da yawa sai dai a kiyasta.

Kafin ka fara fim ko akwai abin da ya fara baka tsoro ga masana’antar?
Babu wani abu daya bani tsoro wallahi.

Za mu ci gaba a mako mai zuwa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kambama Marubutan Kasar Sin A Babban Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Hugo

Next Post

Gwamnan Kano ya buÉ—e Cibiyar Hadda da Nazarin AlÆ™ur’ani A Gidan Kwankwaso

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

5 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

7 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

2 weeks ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

3 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

4 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Kwankwaso

Gwamnan Kano ya buɗe Cibiyar Hadda da Nazarin Alƙur'ani A Gidan Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke YaÉ—uwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke YaÉ—uwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Muhammadu Murtala

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.