• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin APC A Katsina: Idan Ba A Dauki Mataki Ba, Jam’iyyar Na Iya Zubar Da Ciki A 2023

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
in Siyasa
0
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon rikicin da ya kunno kai a Jami’yyar APC tun bayan kammala zaben fid da gwani da aka gudanar, na neman zama wata sabuwar hanyar da ka iya kai jamiyyar rijiya gaba dubu (wanda ya fada ya tafi kenan).

Yanzu haka dai masana na ci gaba da yin sharhi a kan wannan matsala da take neman raba jamiyyar APC gida biyu a Jihar Katsina bayan musayar kalamai da ke tada kura daga bangarori biyu.

  • Kudirin Ba Dalibai Rancen Kudi Mara Ruwa Ya Tsallake Karatu Na 2 A Zauren Majalisar Dattijai

Mukadashin shugaban tsangayar siyasa a Jami’ar Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina, Dakta Kabir Musa Yandaki ya jaddada cewa matukar ba a dauki mataki cikin sauri ba, makomar APC a Katsina shi ne tana iya dafa kasa ko ma ta zubar da ciki wato dai faduwar zaben da za a yi.

Ya kara da cewa ita jami’yyar a irin wannan lokaci babu abin da take bukata kamar dinke duk wata baraka da rikicin cikin gida, domin fuskantar zabe da sauran jam’iyyun siyasa da ke dakun karawa da ita.

“Maganar da mataimakin shugaban jam’iyyar APC na Jihar Katsina, Bala Abubakar Musawa ya yi, magana ce mai tsadar gaske a irin wannan lokaci da ake neman jama’a ba wai a kore su ba kamar yadda ya yi barazana,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Sulhun PDP Ya HaÉ—u Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

Bala Abu Musawa dai an ruwaito shi a gaban Gwamna Aminu Bello Masari a karamar hukumar Malumfashi inda suka je bude wasu ayyuka, ya furta cewa ko APC za ta fadi zabe sai sun hukunta wadanda suke halartar wasu tarurruka da suka yi zargin ana cin mutuncin Buhari da Gwamna Masari.

Tun kafin Bala ya yi wannan martani, tsohon sakataran gwamnatin Jihar Katsina kuma daya daga cikin wadanda suka nemi takarar gwamnan jihar bai samu nasara ba, Dakta Mustapha Inuwa ya yi wani taro da kungiyoyi da magoya bayansa, inda ya yi wasu maganganu da ake ganin ya kasa nuna juriya a siyasa.
Daga cikin maganganun da Dakta Mustapha Inuwa ya yi ya ce, an ci amanarsa, sai dai kai-tsaye bai kira sunan wanda ya ci amanarsa ba, amma dai masu sharhi siyasa na ganin wannan magana tasa da Gwamna Aminu Bello yake yi.

Sannan Dakta Mustapha ya kara da cewa duk wani magoyin bayansa da aka yi wa ba daidai ba a cikin jamiyyar APC, to duk inda ya koma zai taimaka masa, batun da ake ganin kamar ya shirya yi wa jam’iyyar APC zagon kasa.

Duk da irin zafin da Dakta Mustapha Inuwa ya dauka sai da ya kara jaddada cewa ya karbi wannan sakamakon a matsayin kaddararsa, sai dai a cewarsa hakan ba yana nufin idan an yi maka ba daidai ba ko magoya bayanka, kuma a ce ba za su yi magana ba.

Babu shakka, ba wanda yake ja da cewa Dakta Mustapha Inuwa bai san tsari da kuma yadda ake tafiyar da siyasar Katsina ba, ya fada da bakinsa wanda ake ganin maganar a matsayin gori, inda ya ce gwamna bai san yadda ake cin zabe ba, sai dai a kawo masa sakamakon zaben an cinye duka.

Sannan ya kara jefa wani kalubale kamar yadda ya saba fada a wasu tarurruka cewa tun da aka ba shi mukamin Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina na tsawan shekara bakwai ya rike amana ba a taba hada baki da shi aka yi rashin gaskiya ba, idan kuma an yi bai yafe wa duk wanda ya rufa masa asiri ba.

A wani bangare na maganganun da suka harzuka Bala Abu har ya yi wancan martani, akwai wasu kalamai da daya daga cikin dakurun gwagwarmayar neman takarar Mustapha Inuwa, tsohon shugaban jam’iyyar APC kuma sakatare a yanzu Malam Shitu Maslaha ya yi.

A cikin jawabin da ya yi a wajan wannan taron, ya yi takaicin yadda masu zaban fid da gwani suka ki zaban dan takararsa, inda a karshe ya ce kashi 70 daga cikinsu (daligetet) jahilai ne.
Malam Shitu Maslaha ya ci gaba da cewa daman ya ji tsoron ka da wannan tafiya ta su ta yi irin karkon siyasar Buhari, wato ya fara da farin jini amma zai kare da zagi, wadannan kalamai da Dakta Mustapha Inuwa da Shitu Maslaha su ne musababin wancan magana ta Bala Abu Musawa.

Tun da farko kafin Shitu Maslaha ya fara jawabi, ya yi bayanin cewa ya mika ne a wannan wuri a matsayinsa na dan gwagwarmayar neman takarar Dakta Mustapha Inuwa ba a matsayinsa na sakataren jam’iyar APC na Jihar Katsina ba.

Saboda haka ya ci gaba da baro bayanai masu kama da zazzage abin da ke cikinsa na yadda suka ji bayan kammala zaben fid da gwani wanda ya zargi Gwamna Aminu Bello Masari kan ya mara wa Dikko Umar Radda baya.

Hakikka daga jin yadda Shitu Maslaha ke magana ka san ya sha ta dubu, wato dai komi zai faru sai dai ya faru, har tarihin siyasarsa ya bayar da irin tsawon lokacin da ya dauka yana adawa, kuma kamar ya shirya fara wata sabuwar adawar tun da maigidansa ya rasa takara.

Wadannan maganganu sun jefa masana da manazarta masu sharhi a kan harkokin siyasa jihar, sabon nazari da karatun ta nutsu a bangaren siyasar Jihar Katsina da kuma makomar ta a zaben 2023.

Kamar yadda Dakta Kabir Musa Yandaki ya fada cewa, ita jami’yya tana da tsarin da take bi wajan hukunta ‘ya’yanta idan sun yi ba daidai ba, amma maganar cewa ko za a fadi zabe sai an hukunta masu halartar irin wancan taro ba daidai ba ne a siyasa.

Ya kuma kara da cewa wannan rikicin cikin gida ne wanda ya kamata a ce Gwamna Aminu Bello Masari ya yi wa tufkar hanci tun kafin abin ya yi nisa, inda ya ce idan aka ci gaba da wannan rikicin cikin gida, to karshe magana shi ne faduwa zabe za a yi ba tare da wata tantanma ba.

A cewar Dakta Kabir Musa Yandaki, su sauran jam’iyyu wannan fadan yana yi masu dadi kuma ba sa so ya kare, domin idan aka ci gaba su za su amfan ta hanyar yi wa jam’iyyar APC dukan kawo wuka a zaben 2023.

Idan ba a manta ba, lokacin da ake tafka shari’a tsakanin Gwamna Aminu Masari da Lado Danmarke, Bala Abu ya yi irin wannan barazanar inda ya ce za su sa mace ta kori duk wanda suka samu da hannu wajan taimaka wa su Lado a kan batun shari’ar da ake yi da su, amma dai haka maganar ta wuce kamar bikin Sallah.

Babban abin da ya fi ba wasu mamaki a cikin maganganun Bala Abu shi ne, za a kori duk wanda ya kara halartar wani taro da ake cin mutuncin Buhari da Gwamna Masari, amma bai ce za a kori mai shirya taron ba, tun da an ce za a ci gaba da yin taron daga lokaci zuwa lokaci.

Wannan musayar yawo dai ta haifar da muhawara sosai a kafafen yada labarai na zamani (Social Media), inda wasu daga cikin masu kaunar Gwamna Masari suke kallon wadancan kalamai tamkar raini ne ga shugaba inda har suka fara mai da martani.

Haka a bangaren tsohon sakataran gwamnatin Jihar Katsina su ma sun fara yada bakaken maganganu da ake ganin rashin dacewar su a siyasa. Matukar jam’iyyar APC dai ba ta son barin ciki a zaben 2023 a Jihar Katsina, ya zama wajibi ta lalubo yadda za ta magance wannan matsalar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Safarar Mata Zuwa Kasashen Larabawa Da Turai Ya Zama Ruwan Dare -MDD

Next Post

Yadda Jam’iyyu Suka Sha Gwagwarmayar Fitar Da Mataimakan ‘Yan Takara

Related

Sulhun PDP Ya HaÉ—u Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya HaÉ—u Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

6 hours ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

1 week ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

1 week ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

2 weeks ago
Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir
Ilimi

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

2 weeks ago
Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya
Siyasa

Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

2 weeks ago
Next Post
Yadda Jam’iyyu Suka Sha Gwagwarmayar Fitar Da Mataimakan ‘Yan Takara

Yadda Jam'iyyu Suka Sha Gwagwarmayar Fitar Da Mataimakan 'Yan Takara

LABARAI MASU NASABA

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

May 30, 2025
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

May 30, 2025
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

May 30, 2025
Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

May 30, 2025
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Sulhun PDP Ya HaÉ—u Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya HaÉ—u Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

May 30, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.