ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jam’iyyu Suka Sha Gwagwarmayar Fitar Da Mataimakan ‘Yan Takara

by Khalid Idris Doya
4 years ago
takara

Bayan kammala zabukan fitar da gwanaye na jam’iyyun siyasa musamman APC da ke mulki a Nijeriya da kuma PDP da ta yunkura take son kwace mulki a yayin babban zaben 2023 da ke tafe.

Wanda hakan ya tabbatar da Asiwaju Bola Ahmad Tinubu daga yankin Kudu a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC da kuma Atiku Abubakar daga Arewa Maso Gabas a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, sai kuma kallo ya karkata zuwa kan su waye za su zaba a matsayin mataimaka.

  • 2023: Tinubu Ya Zabi Kabir Ibrahim Masari Daga Katsina A Matsayin Mataimakinsa

Kazalika, sauran jam’iyyun irinsu NNPP ta tsayar da tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso ne a matsayin dan takararta.

ADVERTISEMENT

Wakilinmu ya labarto cewa manyan jam’iyyu biyun sun sha kwaranniya kan yadda za su zabi mataimaka, lamarin da ya sanya ‘yan takaran suka shiga tsaka mai wuya na neman mataimaka musamman ma a jam’iyyar APC.

A bisa lura da yadda siyasar kasar nan ke tafiya, ana duba shugaba daga wani yanki ya fito kana a zabi mataimaki daga wata yanki domin tabbatar da tafiya da kowani yanki cikin sha’anin mulki da shugabanci.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A jam’iyyar APC dai Bola Ahmad Tinubu ya fito karara ya nuna cewa iko da dammar zabar mataimakin shugaban kasa na hannunsa ne, kan hakan ne ake kyautata zaton zai dauki dan arewa maso gabas kuma kirista. Kodayake ya sha kusa dangane da tunanin da wasu ke yi na cewa zai iya zabar musulmi kuma daga yankin arewa a matsayin mataimakinsa.

Domin neman hadin kai da cigaban jam’iyyar, masu ruwa da tsaki na APC sun yi tir da matakin daukan musulmi a matsayin mataimaki lura da cewa Bola Tinubu musulmi ne da ya zama dan takara, sun dan nace kan cewa dole ne Tinubu ya dauki kirista kuma daga yankin arewa.

A dai yau Juma’a 17 ga watan June wa’adin da hukumar zabe ta bai wa jam’iyyu na su gabatar mata da sunayen ‘yan takata da mataimakansu. Kan hakan ne suka bazama neman mataimaka.
A wata hira da aka yi da gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, ya bayyana cewar damar zabar mataimakin shugaban kasa na hannun Tinubu ne. Ya ce, babu inda aka bayyana cikin kundin tsarin mulkin kasa cewa dole ne sai Musulmi ya dauki kirista a matsayin mataimakinsa, ya ce kawai sai ana yin hakan ne domin cigaba da kuma hadin kai a tsakanin yankunan kasar nan.

Bisa kin amincewa da wasu masu ruwa da tsaki suka yi na tikitin Musulmi da Musulmi, hakan ta sanya ake kyautata zaton Tinubu zai iya daukar tsohon Kakakin Majalisar tarayya, Honorable Yakubu Dogara a matsayin mataimakinsa.

Dogara dai kirista ne kuma ya fito ne daga yankin Arewa Maso Gabas, don haka ne ake harsashen zai iya samun wannan damar.

Kodayake bayan Dogara, akwai wasu da ake ganin Tinubu zai iya zaba kamar su Simon Lalong na jihar Filato da Nasir El-Rufa’i na Kaduna da kuma Muhammad Badaru Abubakar na Jigawa. Da kuma gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum, da kuma tsohon gwamnan Benue George Akume. Amma harsashe ya fi karfi kan Dogara dan asalin jihar Bauchi.

Kodayake daga fari Gwamnonin APC Sun so zabar wa Tinubu mataimaki, amma hakan bai samu ba, inda alamu suka nuna Tinubu da jam’iyyar APC za su yi gaban kansu ne su dubi wanda suke ganin zai iya kawo musu kuri’a da za su iya cin zabe ba tare da duba addini ko bangaren da ya fito ba.

A bangaren jam’iyyar PDP kuwa, ana kyautat zaton cewa Atiku Abubakar zai zabi gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ne a matsayin mataimakinsa da za su yi takarar 2023 a tare.

Ana tunanin Atiku Abubakar zai zabi Wike ne domin cike kibin siyasa da kuma kasancewarsa dan yankin Kudu, lura da cewa shi Atiku ya fito daga yankin Arewa.
Wike dai ya fito neman tikitin Shugaban kasa a jam’iyyar PDP inda Atikun ya kayar da shi da kuri’u 371 yayin da shi kuma Wike din ya samu kuri’u 237 a zaben fitar da gwani da suka gudanar kwanakin baya a Abuja.

Bayan Wike akwai rade-radin cewa jam’iyyar da dan takararta Atiku Abubakar na shirin daukar tsohon gwamnan Imo Emeka Ihedioha.
Kazalika NNPP da ta tsayar da Rabi’u Musa Kwankwaso akwai yiwuwar ta dauko nata mataimakin daga Kudanci.

takara
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
‘El-Rufa’i Ya Cancanci Yabo Wajen Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba’

'El-Rufa’i Ya Cancanci Yabo Wajen Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba'

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.