ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jam’iyyu Suka Sha Gwagwarmayar Fitar Da Mataimakan ‘Yan Takara

by Khalid Idris Doya
4 years ago
takara

Bayan kammala zabukan fitar da gwanaye na jam’iyyun siyasa musamman APC da ke mulki a Nijeriya da kuma PDP da ta yunkura take son kwace mulki a yayin babban zaben 2023 da ke tafe.

Wanda hakan ya tabbatar da Asiwaju Bola Ahmad Tinubu daga yankin Kudu a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC da kuma Atiku Abubakar daga Arewa Maso Gabas a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, sai kuma kallo ya karkata zuwa kan su waye za su zaba a matsayin mataimaka.

  • 2023: Tinubu Ya Zabi Kabir Ibrahim Masari Daga Katsina A Matsayin Mataimakinsa

Kazalika, sauran jam’iyyun irinsu NNPP ta tsayar da tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso ne a matsayin dan takararta.

ADVERTISEMENT

Wakilinmu ya labarto cewa manyan jam’iyyu biyun sun sha kwaranniya kan yadda za su zabi mataimaka, lamarin da ya sanya ‘yan takaran suka shiga tsaka mai wuya na neman mataimaka musamman ma a jam’iyyar APC.

A bisa lura da yadda siyasar kasar nan ke tafiya, ana duba shugaba daga wani yanki ya fito kana a zabi mataimaki daga wata yanki domin tabbatar da tafiya da kowani yanki cikin sha’anin mulki da shugabanci.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

A jam’iyyar APC dai Bola Ahmad Tinubu ya fito karara ya nuna cewa iko da dammar zabar mataimakin shugaban kasa na hannunsa ne, kan hakan ne ake kyautata zaton zai dauki dan arewa maso gabas kuma kirista. Kodayake ya sha kusa dangane da tunanin da wasu ke yi na cewa zai iya zabar musulmi kuma daga yankin arewa a matsayin mataimakinsa.

Domin neman hadin kai da cigaban jam’iyyar, masu ruwa da tsaki na APC sun yi tir da matakin daukan musulmi a matsayin mataimaki lura da cewa Bola Tinubu musulmi ne da ya zama dan takara, sun dan nace kan cewa dole ne Tinubu ya dauki kirista kuma daga yankin arewa.

A dai yau Juma’a 17 ga watan June wa’adin da hukumar zabe ta bai wa jam’iyyu na su gabatar mata da sunayen ‘yan takata da mataimakansu. Kan hakan ne suka bazama neman mataimaka.
A wata hira da aka yi da gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, ya bayyana cewar damar zabar mataimakin shugaban kasa na hannun Tinubu ne. Ya ce, babu inda aka bayyana cikin kundin tsarin mulkin kasa cewa dole ne sai Musulmi ya dauki kirista a matsayin mataimakinsa, ya ce kawai sai ana yin hakan ne domin cigaba da kuma hadin kai a tsakanin yankunan kasar nan.

Bisa kin amincewa da wasu masu ruwa da tsaki suka yi na tikitin Musulmi da Musulmi, hakan ta sanya ake kyautata zaton Tinubu zai iya daukar tsohon Kakakin Majalisar tarayya, Honorable Yakubu Dogara a matsayin mataimakinsa.

Dogara dai kirista ne kuma ya fito ne daga yankin Arewa Maso Gabas, don haka ne ake harsashen zai iya samun wannan damar.

Kodayake bayan Dogara, akwai wasu da ake ganin Tinubu zai iya zaba kamar su Simon Lalong na jihar Filato da Nasir El-Rufa’i na Kaduna da kuma Muhammad Badaru Abubakar na Jigawa. Da kuma gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum, da kuma tsohon gwamnan Benue George Akume. Amma harsashe ya fi karfi kan Dogara dan asalin jihar Bauchi.

Kodayake daga fari Gwamnonin APC Sun so zabar wa Tinubu mataimaki, amma hakan bai samu ba, inda alamu suka nuna Tinubu da jam’iyyar APC za su yi gaban kansu ne su dubi wanda suke ganin zai iya kawo musu kuri’a da za su iya cin zabe ba tare da duba addini ko bangaren da ya fito ba.

A bangaren jam’iyyar PDP kuwa, ana kyautat zaton cewa Atiku Abubakar zai zabi gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ne a matsayin mataimakinsa da za su yi takarar 2023 a tare.

Ana tunanin Atiku Abubakar zai zabi Wike ne domin cike kibin siyasa da kuma kasancewarsa dan yankin Kudu, lura da cewa shi Atiku ya fito daga yankin Arewa.
Wike dai ya fito neman tikitin Shugaban kasa a jam’iyyar PDP inda Atikun ya kayar da shi da kuri’u 371 yayin da shi kuma Wike din ya samu kuri’u 237 a zaben fitar da gwani da suka gudanar kwanakin baya a Abuja.

Bayan Wike akwai rade-radin cewa jam’iyyar da dan takararta Atiku Abubakar na shirin daukar tsohon gwamnan Imo Emeka Ihedioha.
Kazalika NNPP da ta tsayar da Rabi’u Musa Kwankwaso akwai yiwuwar ta dauko nata mataimakin daga Kudanci.

takara
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
‘El-Rufa’i Ya Cancanci Yabo Wajen Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba’

'El-Rufa’i Ya Cancanci Yabo Wajen Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba'

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.