• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Gaza: Ana Ci Gaba Da Tir Da Kisan Fararen Hula A Harin Asibiti

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Gaza

Kasashen duniya na ci gaba da tofin Allah-tsine kan harin da ya janyo kisan daruruwan fararen hula a wani asibitin Gaza da ake zargin isra’ila da kaiwa.

Duk kokarin da kasashen duniya ke yi na ganin an samu maslaha kan rikicin Gaza, da alama abin ya ci tura sakamakon yadda ake dada samun rarrabuwar kawuna tsakanin masu tausayin Falasdinawa da magoya bayan Yahudun Isra’ila.

  • Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina
  • Sin Ta Kafa Kyakkyawan Misali A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

A wannan makon, an soke ganawar Shugaban Amurka Joe Biden da wasu shugabanni na Kungiyar Hadin Kan Larabawa a kasar Jordan.

Wakazalika, kasashen duniya masu tausayin Falasdinawa sun mara baya ga wani kudiri na tsagaita wuta da kasar Brazil ta gabatar wa zauren Majalizar Dinkin Duniya, sai dai Amurka ta hau kujerar na-ki a kan tabbatar da aiki da kudirin bisa abin da ta ce “ba a yi wa Isra’ila adalci ba a ciki”.

Kasashen Asiya sun yi hannun riga da na Turai kan yakin da ake yi a Zirin Gaza.

LABARAI MASU NASABA

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

…Masar Ta Bude Kan Iyakarta Da Gaza Domin Kai Taimako
Rahotanni daga kafofin yada labarai sun bayyana cewa Masar ta bude iyakarta da Gaza na wani dan lokaci domin bari a shigar da kayan agaji da kuma kyale ‘yan kasashen waje su fita.

Sai dai Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ba ta tabbatar da rahotannin ba.
Wani sako da aka wallafa a shafin sada zumunta, ya bai wa Amurkawa da ke Gaza shawarar cewa su matsa kusa da iyakar Rafah idan suka tabbatar babu wani hadari.
A ranar Laraba ne Shugaban Amurka ya kai ziyara Isra’ila a karon farko tun bayan harin da Hamas ta kai a ranar 7 ga wannan watan.

…Harin Asibitin Gaza: Shugaban Amurka Ya Wanke Isra’ila
A lokacin da yake ganawa da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, Shugaba Amurka, Joe Biden ya danganta harin makamai da aka kai a wani asibitin Gaza ranar Talata ga Falasdinawa cewa ba Isra’ila ba ce, bisa bayanan da ya samu inda Biden ya ce a cikin kalamansa – ‘dayan bangaren ne’.

Wannan lamari dai ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a a yankin tare da soke taron da aka shirya yi tsakanin shugaba Biden da shugabannin kasashen Larabawa.

Shugaban ya jajanta wa Isra’ila game da harin da Hamas ta kai amma ya jaddada mahimmancin rage asarar fararen hula.
Wakilin Falasdinawa a Majalisar Dinkin Duniya, Riyad Mansoor ya nemi Amurka ta dakatar da Isra’ila kan kisan da take yi a Gaza, bayan harin asibitin da ake zargin ta kai ya hallaka fiye da fararen hula 450 zuwa ranar Laraba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Next Post
Magajin garin Zazzau

Gwamna Uba Sani Ya Mika Ta'aziyya Ga Iyalan Marigayi Magajin Garin Zazzau

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.