• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Gaza: Ana Ci Gaba Da Tir Da Kisan Fararen Hula A Harin Asibiti

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Rikicin Gaza: Ana Ci Gaba Da Tir Da Kisan Fararen Hula A Harin Asibiti
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashen duniya na ci gaba da tofin Allah-tsine kan harin da ya janyo kisan daruruwan fararen hula a wani asibitin Gaza da ake zargin isra’ila da kaiwa.

Duk kokarin da kasashen duniya ke yi na ganin an samu maslaha kan rikicin Gaza, da alama abin ya ci tura sakamakon yadda ake dada samun rarrabuwar kawuna tsakanin masu tausayin Falasdinawa da magoya bayan Yahudun Isra’ila.

  • Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina
  • Sin Ta Kafa Kyakkyawan Misali A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

A wannan makon, an soke ganawar Shugaban Amurka Joe Biden da wasu shugabanni na Kungiyar Hadin Kan Larabawa a kasar Jordan.

Wakazalika, kasashen duniya masu tausayin Falasdinawa sun mara baya ga wani kudiri na tsagaita wuta da kasar Brazil ta gabatar wa zauren Majalizar Dinkin Duniya, sai dai Amurka ta hau kujerar na-ki a kan tabbatar da aiki da kudirin bisa abin da ta ce “ba a yi wa Isra’ila adalci ba a ciki”.

Kasashen Asiya sun yi hannun riga da na Turai kan yakin da ake yi a Zirin Gaza.

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

…Masar Ta Bude Kan Iyakarta Da Gaza Domin Kai Taimako
Rahotanni daga kafofin yada labarai sun bayyana cewa Masar ta bude iyakarta da Gaza na wani dan lokaci domin bari a shigar da kayan agaji da kuma kyale ‘yan kasashen waje su fita.

Sai dai Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ba ta tabbatar da rahotannin ba.
Wani sako da aka wallafa a shafin sada zumunta, ya bai wa Amurkawa da ke Gaza shawarar cewa su matsa kusa da iyakar Rafah idan suka tabbatar babu wani hadari.
A ranar Laraba ne Shugaban Amurka ya kai ziyara Isra’ila a karon farko tun bayan harin da Hamas ta kai a ranar 7 ga wannan watan.

…Harin Asibitin Gaza: Shugaban Amurka Ya Wanke Isra’ila
A lokacin da yake ganawa da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, Shugaba Amurka, Joe Biden ya danganta harin makamai da aka kai a wani asibitin Gaza ranar Talata ga Falasdinawa cewa ba Isra’ila ba ce, bisa bayanan da ya samu inda Biden ya ce a cikin kalamansa – ‘dayan bangaren ne’.

Wannan lamari dai ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a a yankin tare da soke taron da aka shirya yi tsakanin shugaba Biden da shugabannin kasashen Larabawa.

Shugaban ya jajanta wa Isra’ila game da harin da Hamas ta kai amma ya jaddada mahimmancin rage asarar fararen hula.
Wakilin Falasdinawa a Majalisar Dinkin Duniya, Riyad Mansoor ya nemi Amurka ta dakatar da Isra’ila kan kisan da take yi a Gaza, bayan harin asibitin da ake zargin ta kai ya hallaka fiye da fararen hula 450 zuwa ranar Laraba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuGazaHamas
ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

Gwamna Uba Sani Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Magajin Garin Zazzau

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

1 hour ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

2 hours ago
Gaza
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

3 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

5 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

5 hours ago
Gaza
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

8 hours ago
Next Post
Magajin garin Zazzau

Gwamna Uba Sani Ya Mika Ta'aziyya Ga Iyalan Marigayi Magajin Garin Zazzau

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Gaza

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Gaza

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.