• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Kabilanci: An Gudanar Da Taron Yafe Wa Juna A Jihar Filato

bySadiq
3 years ago
Filato

Gwamnatin Jihar Filato ta jagoranci wani gagarumin taro a birnin Jos domin yafe wa juna da kuma sasanta al’ummar jihar da rikicin kabilanci da Addini ya raba kawunansu.

Wannan biki ya gudana ne a karkashin jagorancin gwamnan jihar, Simon Bako Lalong wanda ya samu halartar Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar II da Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da shugaban mabiya darikar Katolika na Nijeriya, Arch Bishop John Onayekan da ya samu wakilcin Arch Bishop Ignatius Kaigama.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo
  • Zan Tabbatar Da An Ci Gajiyar Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe Muddin Aka Zabe Ni – Atiku

Yayin gudanar da jawabinsa, gwamna Lalong wanda ya bayyana farin cikinsa da yadda jama’a suka amsa kiran da ya musu, ya ce sun yi nasarar kafa ginshikin zaman lafiya da adalci da mutunta juna da kuma karbar baki.

Lalong, ya ce da taimakon sarakunan gargajiya da limaman Addinai da shugabannin al’umma, gwamnatinsa ta yi aiki tukuru wajen sake fasalin jihar da kuma hada kan jama’a.

Gwamnan, ya ce kokarin da suka yi, ya taimaka wajen kawar da tsoro da rashin amincewa juna da kuma kyamar da ake samu a tsakanin jama’ar jihar da suka fito daga kabilu daban-daban

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Lalong ya bukaci jama’ar Jihar Filato da su rungumi shirin yafe wa juna da kuma hadin kai, yayin da shi ma ya nemi gafarar jama’ar da suke zaton ya saba musu.

Yayin jawabinsa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Saad Abubakar, ya jinjina wa gwamnatin Jihar Filato saboda jajircewar da ta yi wajen ganin ta tabbatar da dorewar zaman lafiya, musamman ganin yadda zaman lafiya da walwala ke dawowa a tsakanin al’umma.

Sarkin Musulmin ya ce babu dalilin da zai sa bayan an kwashe shekaru aru-aru ana zaman lafiya a Jihar, a ce kuma yanzu wasu ‘yan tsiraru za su hana zaman lafiya, yayin da ya gargadi jama’a da su daina barin bata gari suna tunzira su domin tashin hankali ba.

A nashi jawabin, Arch Bishop Ignatius Kaigama, shugaban mabiya darikar Katolika ya bayyana farin cikinsa cewar kokarin da suka yi a Filato na tabbatar da zaman lafiya ya kankama, sakamakon rawar da gwamnatin jihar ta taka.

Shugaban sarakunan Jihar Filato, Gbong Gwom Jos, Jacob Gyang Buba, ya bayyana taron a matsayin mai dimbin tarihi, saboda yadda ya tabbatar da aniyar Gwamna Lalong na janyo hankalin jama’ar jihar domin watsi da matsalolin da aka samu a baya dan rungumar zaman lafiya.

Cikin wadanda suka halarci bikin har da tsofaffin gwamnonin Jihar, Janar Lawrence Onoja mai ritaya da Sir Fidelis Tapgun.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC

2023: Mun Fara Horas Da Ma'aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 - INEC

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version