• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta fara aikin horas da ma’aikatan da za su yi aikin zaɓen 2023 a cikin Fabrairu da Maris.

 

Ma’aikatan na wucin-gadi su miliyan 1 ne da 265,227, kamar yadda Babban Jami’in Wayar da Kai kuma Kwamishina na INEC, Mista Festus Okoye, ya bayyana a ranar Litinin, a wurin bayar da wani horon a ranar Litinin.

  • CBN Ya Tabbatarwa INEC Samun Wadatattun Takardun Naira Don Gudanar Da Zaben 2023

Ya ce hukumar ta ɗauki wannan horaswa da muhimmanci, ganin cewa Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, Farfesa Mahmood Yakubu ya sha alwashin tabbatar da an gudanar da sahihin zaɓe, karɓaɓɓe, kuma wanda jama’a za su yi tururuwar fita su jefa ƙuri’a.

 

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Okoye ya ƙara cewa haka kuma wannan zaɓe mai zuwa, zaɓe ne wanda za a yi amfani da na’urar fasaha a wurin zaɓe.

 

Ya yi tsinkayen cewa aikin ofishin sa ne wanda aka ɗora wa haƙƙin shawartar Kwamishinonin Zaɓe na Jihohi (REC) da jami’an zaɓe hanyoyin da su ka fi dacewa su fahimtar da jama’a batutuwan da su ka danganci amfani da na’urorin fasaha a lokacin zaɓe.

INEC

Ya ƙara da cewa a ranakun 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris ‘yan Nijeriya za su zaɓi shugaban ƙasa, sanatoci 109, mambobin majalisar wakilai su 360, gwamnoni 28, sai mambobin majalisar dokoki 993.

 

Ya ce mutum miliyan 93 da 469,008 ne su ka yi rajistar katin zaɓe, kuma ake sa ran za su fita su jefa ƙuri’a a ranakun 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris.

 

Ya ce: “Zaɓen 2023 zai tafi ne a bisa tsarin amfani da na’urar fasahar zamani. INEC za ta yi amfani da na’urar tantance masu katin shaidar rajistar zaɓe, wato BVAS a dukkan rumfunan zaɓe 176,846 a ƙasar nan.

 

“Kuma INEC ta yi gwajin waɗannan na’urorin, wato BVAS ta tabbatar da ingancin su. Yanzu haka ana ci gaba da ba su lambobin tantance mai katin shaidar rajistar zaɓe, ta yadda za su kasance lambobin sun zama mabiyi da mabiyi, ko ɗaya bayan ɗaya a lokacin zaɓe.”

 

A cewar Okoye, Sashen Dokar Zaɓe na 47(2) ya tilasta cewa babu wanda zai yi zaɓe ba tare da an tantance shi na BVAS ba.

 

Ya ƙara da cewa: “Za a yi amfani da baturen zaɓe 707, 384 da su ka haɗa da mataimakan su. Sai kuma wasu ma’aikata 17,685 a matsayin turawan zaɓe masu sa-ido, jami’an tattarawa da bayyana sakamakon zaɓe su 9,620, sai kuma jami’an tsaron rumfunan zaɓe su 530,538. Ya ce gaba ɗaya idan an haɗa, sun cika 1,265,227 kenan.

 

Dukkan waɗannan su na ci gaba da samun horon sanin makamar aiki, yayin da nan da ‘yan kwanaki za a ci gaba da bayar da horon ga saura, inji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Kabilanci: An Gudanar Da Taron Yafe Wa Juna A Jihar Filato

Next Post

An Ciro Wata Mata Da Rai Daga Baraguzai Bayan Shafe Awa 52 A Turkiyya

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

2 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

4 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

4 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

6 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

11 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

12 hours ago
Next Post
An Ciro Wata Mata Da Rai Daga Baraguzai Bayan Shafe Awa 52 A Turkiyya

An Ciro Wata Mata Da Rai Daga Baraguzai Bayan Shafe Awa 52 A Turkiyya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.