Yayin da ake tsaka da rikicin masarautar Kano, Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya daga tutar mulki a karamar fadar da ke Nassarawa.
Wannan yana nuna iko da Sarkin yake da shi a yanzu.
- Farfesa Aisha Maikudi Ta Zama Mukaddashiyar Shugaban Jami’ar Abuja
- Rasuwar Suruka: Gwamnoni Sun Kai Wa Shettima Ziyarar Ta’aziyya
A bisa al’ada, tutar na zama ne a matsayin alamar iko, kuma daga ta na alamta cewa sarki yana cikin fada.
Wannan kuwa na zuwa ne duk da umarnin gwamnatin Kano ga Sarki Aminu ya fice daga fadar a yayin da ake ci gaba da dambarwar sarautar Kano.
Akan daga tutar ce da misalin karfe 6 na safe a kuma sauke ta 6 na yamma ko idan sarki ya yi bulaguron aiki.
Kano ta shiga rikicin masarauta tun bayan da gwamnatin jihar ta rushe masarautun Bichi, Karaye, Rano da Gaya wanda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ya kirkiro.
Rikicin na ci gaba da haifar da rudani yayin da Aminu Ado Bayero da Sarkin Kano na 14, Muhammdu Sanusi II kowa ke ci gaba da ikirarin shi ne Sarkin Kano.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp