ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Tsagin Ganduje Ne Silar Hana Tinubu Aike Wa Majalisa Sunan Minista Daga Kano

by Muhammad
2 years ago
Ganduje

A makon da ya gabata ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya mika sunayen ministoci 28, ban da wasu jihohi 11 ciki har da Kano.

Wata majiya ta bayyana wa NIGERIA TRACKER cewa tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya dage kan mika sunan, Injiniya Rabi’u Suleiman Bichi daga Kano.

  • Ganduje Ya Aike Da Sunan Gawuna A Masa Mukamin Minista
  • Dalilin Da Ya Sa Tinubu Bai Bawa Kano Mukamin Minista Ba

Sai dai kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Kano, Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna, shi ma yana matsa lamba kan a saka sunansa cikin jerin sunayen da za a mikawa majalisar dattawa domin tantancewa.

ADVERTISEMENT

Majiyar ta kara da cewa a yanzu dan takarar Gwamna na jam’iyyar APC ya aike da wasu wakilansa zuwa wajen Gwamna Ganduje, inda suka bukace shi da ya mika sunan Gawunan a matsayin minista daga Kano.

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa, Shugaba Bola Ahmad Tinubu, ya yi alkawarin ba wa Kano mukaman minista guda biyu, daya daga tsagin Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, da daya kuma daga tsagin Jagoran Gandujiyya kuma tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

LABARAI MASU NASABA

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Tun da Ganduje ba zai samu shiga cikin kunshin ministocin Shugaba Tinubu ba, shugaban kasar ya ba shi damar kawo minista, wanda a yanzu haka ya janyo cece-kuce a da’irar siyasar tsohon Gwamna Ganduje.

Majiyar ta kuma sanar da NIGERIAN TRACKER cewa idan shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya mika sunayen ministoci na gaba daga Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da kuma wani mutum daya daga tsagin Ganduje ne da ya mika.

Wata majiya ta ce, tsagin rusasshiyar jam’iyyar ACN a Kano, karkashin jagorancin shugaba Tinubu a zabukan 2007 da 2011, na matse lamba wajen nada dan takarar gwamna na jam’iyyar a 2011 kuma tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano. Injiniya Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo.

Dalilan da tsaffin jiga-jigan jam’iyyar ACN suka bayar na cewa shugaba Tinubu ya nada ATM Gwarzo a cikin majalisarsa, shi ne, shugaba Tinubu ya yi fice wajen bayar da ladan siyasa, kuma kasancewarsa amininsa na tuntuni, don haka Injiniya Gwarzo yana cikin wadanda suka fi cancantar zama minista a Kano.

Don haka ana sa ran shugaba Tinubu zai tuntubi tsagin tsohon gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau, duk da cewa a halin yanzu yana PDP, saboda rawar da ya taka wajen kafa APC a 2011.

Majiyar ta kuma bayyana cewa, shugaba Tinubu ba shi da gaggawar nada ministoci daga Kano, don akwai yuyuwar kafin nadin ministocin zai tuntubi Sarkin Kano na 14, kafin ya mika sunayen daga Kano.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa
Siyasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP
Siyasa

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Next Post
Harin ‘Yan Bindiga: Gwamna Bago Ya Jajanta Wa Al’ummar Masarautar Kagara

Harin ‘Yan Bindiga: Gwamna Bago Ya Jajanta Wa Al’ummar Masarautar Kagara

LABARAI MASU NASABA

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

November 15, 2025
Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

November 15, 2025
Yadda Za Ku Gyara Kanku

Yadda Za Ku Gyara Kanku

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.