• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Tsagin Ganduje Ne Silar Hana Tinubu Aike Wa Majalisa Sunan Minista Daga Kano

by Muhammad
2 years ago
Ganduje

A makon da ya gabata ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya mika sunayen ministoci 28, ban da wasu jihohi 11 ciki har da Kano.

Wata majiya ta bayyana wa NIGERIA TRACKER cewa tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya dage kan mika sunan, Injiniya Rabi’u Suleiman Bichi daga Kano.

  • Ganduje Ya Aike Da Sunan Gawuna A Masa Mukamin Minista
  • Dalilin Da Ya Sa Tinubu Bai Bawa Kano Mukamin Minista Ba

Sai dai kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Kano, Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna, shi ma yana matsa lamba kan a saka sunansa cikin jerin sunayen da za a mikawa majalisar dattawa domin tantancewa.

Majiyar ta kara da cewa a yanzu dan takarar Gwamna na jam’iyyar APC ya aike da wasu wakilansa zuwa wajen Gwamna Ganduje, inda suka bukace shi da ya mika sunan Gawunan a matsayin minista daga Kano.

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa, Shugaba Bola Ahmad Tinubu, ya yi alkawarin ba wa Kano mukaman minista guda biyu, daya daga tsagin Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, da daya kuma daga tsagin Jagoran Gandujiyya kuma tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Tun da Ganduje ba zai samu shiga cikin kunshin ministocin Shugaba Tinubu ba, shugaban kasar ya ba shi damar kawo minista, wanda a yanzu haka ya janyo cece-kuce a da’irar siyasar tsohon Gwamna Ganduje.

Majiyar ta kuma sanar da NIGERIAN TRACKER cewa idan shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya mika sunayen ministoci na gaba daga Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da kuma wani mutum daya daga tsagin Ganduje ne da ya mika.

Wata majiya ta ce, tsagin rusasshiyar jam’iyyar ACN a Kano, karkashin jagorancin shugaba Tinubu a zabukan 2007 da 2011, na matse lamba wajen nada dan takarar gwamna na jam’iyyar a 2011 kuma tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano. Injiniya Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo.

Dalilan da tsaffin jiga-jigan jam’iyyar ACN suka bayar na cewa shugaba Tinubu ya nada ATM Gwarzo a cikin majalisarsa, shi ne, shugaba Tinubu ya yi fice wajen bayar da ladan siyasa, kuma kasancewarsa amininsa na tuntuni, don haka Injiniya Gwarzo yana cikin wadanda suka fi cancantar zama minista a Kano.

Don haka ana sa ran shugaba Tinubu zai tuntubi tsagin tsohon gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau, duk da cewa a halin yanzu yana PDP, saboda rawar da ya taka wajen kafa APC a 2011.

Majiyar ta kuma bayyana cewa, shugaba Tinubu ba shi da gaggawar nada ministoci daga Kano, don akwai yuyuwar kafin nadin ministocin zai tuntubi Sarkin Kano na 14, kafin ya mika sunayen daga Kano.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Next Post
Harin ‘Yan Bindiga: Gwamna Bago Ya Jajanta Wa Al’ummar Masarautar Kagara

Harin ‘Yan Bindiga: Gwamna Bago Ya Jajanta Wa Al’ummar Masarautar Kagara

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.