• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Tsagin Ganduje Ne Silar Hana Tinubu Aike Wa Majalisa Sunan Minista Daga Kano

by Muhammad
2 years ago
in Siyasa
0
Rikicin Tsagin Ganduje Ne Silar Hana Tinubu Aike Wa Majalisa Sunan Minista Daga Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya mika sunayen ministoci 28, ban da wasu jihohi 11 ciki har da Kano.

Wata majiya ta bayyana wa NIGERIA TRACKER cewa tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya dage kan mika sunan, Injiniya Rabi’u Suleiman Bichi daga Kano.

  • Ganduje Ya Aike Da Sunan Gawuna A Masa Mukamin Minista
  • Dalilin Da Ya Sa Tinubu Bai Bawa Kano Mukamin Minista Ba

Sai dai kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Kano, Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna, shi ma yana matsa lamba kan a saka sunansa cikin jerin sunayen da za a mikawa majalisar dattawa domin tantancewa.

Majiyar ta kara da cewa a yanzu dan takarar Gwamna na jam’iyyar APC ya aike da wasu wakilansa zuwa wajen Gwamna Ganduje, inda suka bukace shi da ya mika sunan Gawunan a matsayin minista daga Kano.

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa, Shugaba Bola Ahmad Tinubu, ya yi alkawarin ba wa Kano mukaman minista guda biyu, daya daga tsagin Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, da daya kuma daga tsagin Jagoran Gandujiyya kuma tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

Labarai Masu Nasaba

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

Tun da Ganduje ba zai samu shiga cikin kunshin ministocin Shugaba Tinubu ba, shugaban kasar ya ba shi damar kawo minista, wanda a yanzu haka ya janyo cece-kuce a da’irar siyasar tsohon Gwamna Ganduje.

Majiyar ta kuma sanar da NIGERIAN TRACKER cewa idan shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya mika sunayen ministoci na gaba daga Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da kuma wani mutum daya daga tsagin Ganduje ne da ya mika.

Wata majiya ta ce, tsagin rusasshiyar jam’iyyar ACN a Kano, karkashin jagorancin shugaba Tinubu a zabukan 2007 da 2011, na matse lamba wajen nada dan takarar gwamna na jam’iyyar a 2011 kuma tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano. Injiniya Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo.

Dalilan da tsaffin jiga-jigan jam’iyyar ACN suka bayar na cewa shugaba Tinubu ya nada ATM Gwarzo a cikin majalisarsa, shi ne, shugaba Tinubu ya yi fice wajen bayar da ladan siyasa, kuma kasancewarsa amininsa na tuntuni, don haka Injiniya Gwarzo yana cikin wadanda suka fi cancantar zama minista a Kano.

Don haka ana sa ran shugaba Tinubu zai tuntubi tsagin tsohon gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau, duk da cewa a halin yanzu yana PDP, saboda rawar da ya taka wajen kafa APC a 2011.

Majiyar ta kuma bayyana cewa, shugaba Tinubu ba shi da gaggawar nada ministoci daga Kano, don akwai yuyuwar kafin nadin ministocin zai tuntubi Sarkin Kano na 14, kafin ya mika sunayen daga Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Katsina Za Ta Dauki Malamai Aiki A Manyan Makarantu

Next Post

Harin ‘Yan Bindiga: Gwamna Bago Ya Jajanta Wa Al’ummar Masarautar Kagara

Related

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 
Siyasa

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

15 hours ago
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
Siyasa

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

20 hours ago
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
Siyasa

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

23 hours ago
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

3 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

3 days ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

3 days ago
Next Post
Harin ‘Yan Bindiga: Gwamna Bago Ya Jajanta Wa Al’ummar Masarautar Kagara

Harin ‘Yan Bindiga: Gwamna Bago Ya Jajanta Wa Al’ummar Masarautar Kagara

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.