• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Tsagin Ganduje Ne Silar Hana Tinubu Aike Wa Majalisa Sunan Minista Daga Kano

by Muhammad
2 years ago
in Siyasa
0
Rikicin Tsagin Ganduje Ne Silar Hana Tinubu Aike Wa Majalisa Sunan Minista Daga Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya mika sunayen ministoci 28, ban da wasu jihohi 11 ciki har da Kano.

Wata majiya ta bayyana wa NIGERIA TRACKER cewa tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya dage kan mika sunan, Injiniya Rabi’u Suleiman Bichi daga Kano.

  • Ganduje Ya Aike Da Sunan Gawuna A Masa Mukamin Minista
  • Dalilin Da Ya Sa Tinubu Bai Bawa Kano Mukamin Minista Ba

Sai dai kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Kano, Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna, shi ma yana matsa lamba kan a saka sunansa cikin jerin sunayen da za a mikawa majalisar dattawa domin tantancewa.

Majiyar ta kara da cewa a yanzu dan takarar Gwamna na jam’iyyar APC ya aike da wasu wakilansa zuwa wajen Gwamna Ganduje, inda suka bukace shi da ya mika sunan Gawunan a matsayin minista daga Kano.

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa, Shugaba Bola Ahmad Tinubu, ya yi alkawarin ba wa Kano mukaman minista guda biyu, daya daga tsagin Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, da daya kuma daga tsagin Jagoran Gandujiyya kuma tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

Labarai Masu Nasaba

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Tun da Ganduje ba zai samu shiga cikin kunshin ministocin Shugaba Tinubu ba, shugaban kasar ya ba shi damar kawo minista, wanda a yanzu haka ya janyo cece-kuce a da’irar siyasar tsohon Gwamna Ganduje.

Majiyar ta kuma sanar da NIGERIAN TRACKER cewa idan shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya mika sunayen ministoci na gaba daga Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da kuma wani mutum daya daga tsagin Ganduje ne da ya mika.

Wata majiya ta ce, tsagin rusasshiyar jam’iyyar ACN a Kano, karkashin jagorancin shugaba Tinubu a zabukan 2007 da 2011, na matse lamba wajen nada dan takarar gwamna na jam’iyyar a 2011 kuma tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano. Injiniya Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo.

Dalilan da tsaffin jiga-jigan jam’iyyar ACN suka bayar na cewa shugaba Tinubu ya nada ATM Gwarzo a cikin majalisarsa, shi ne, shugaba Tinubu ya yi fice wajen bayar da ladan siyasa, kuma kasancewarsa amininsa na tuntuni, don haka Injiniya Gwarzo yana cikin wadanda suka fi cancantar zama minista a Kano.

Don haka ana sa ran shugaba Tinubu zai tuntubi tsagin tsohon gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau, duk da cewa a halin yanzu yana PDP, saboda rawar da ya taka wajen kafa APC a 2011.

Majiyar ta kuma bayyana cewa, shugaba Tinubu ba shi da gaggawar nada ministoci daga Kano, don akwai yuyuwar kafin nadin ministocin zai tuntubi Sarkin Kano na 14, kafin ya mika sunayen daga Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Katsina Za Ta Dauki Malamai Aiki A Manyan Makarantu

Next Post

Harin ‘Yan Bindiga: Gwamna Bago Ya Jajanta Wa Al’ummar Masarautar Kagara

Related

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum
Labarai

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

10 hours ago
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Manyan Labarai

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

1 day ago
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde
Labarai

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

2 days ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

5 days ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

1 week ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

1 week ago
Next Post
Harin ‘Yan Bindiga: Gwamna Bago Ya Jajanta Wa Al’ummar Masarautar Kagara

Harin ‘Yan Bindiga: Gwamna Bago Ya Jajanta Wa Al’ummar Masarautar Kagara

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.