• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Labarai
0
Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Hisba, hukuma ce da ke da hurumi a Shari’ar Musulunci, kasancewar babban aikinta shi ne umarni da aikin alhairi da kuma hani da mummunan aiki, an kaddamar Hukumar Hisba tun lokacin zangon farko na Gwamna Kwankwaso, amma ta samu cikakken gindin zama a shekara ta 2007 zamanin Mulkin Malam Ibrahim Shekaru inda Shugaban Hukumar Hisba na farko shi ne Sheikh Malam Yahaya Farouk Chedi bayan shi Kuma Malam Ibrahimahim Mai bushira.

Hukumar Hisba a Jihar Kano ba yanzu shugabaninta suka fara gamuwa da tunzuri daga wasu mutane da ke ganin aikin na Hisba na yin katsalandan ga sana’unsu ko ra’ayinsu, Malam Abdulkarin Abubakar Rabo wanda har wata wakar cin zarafi taron wasu mawaka suka yi masa saboda kawai ya matsa lamba kan daidaita sahun wasu rukunin al’umma da ake ganin suna kokarin gurbata tarbiyyar yara musamman mata.

  • Kano Za Ta Haɗa Gwiwa Da Afrinvest Don Haɓɓaka Kasuwanci Da Ci Gaban Jihar 
  • Yadda Sheikh Daurawa Ya Koma Ofis Bayan Sulhu Da Gwamnan Kano

Bayan samun sauyin Gwamnati ne kuma Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya sake darewa an karagar mulkin Kano kuma ya nada sabon Shugaban Hukumar ta Hisba Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, wanda kowa ya san shi mai goyon bayan Darikar Kwankwasiyya ne, sannan kowa ya san Daurawa a matsayin wanda ya samar da gagarumin ci gaba a harkokin gudanarwa hukumar, ciki har da nasarar bijiro da shirin auren zawarawa wanda ya dauki hankalin duniya baki daya.

Halin da ake abin ya zama sahun gaba cikin abubuwan da dake daukar hankali a Kano bai wuce batun murabus din Daurawa ba, sakamakon jawabin da Gwamnan ya gabatar a lokacin taron daukacin mala-man addini da limamai da ya gudana a fadar Gwamnatin Kano, inda Gwamnan ya bayyana matakn Hukumar Hisba na yaki da badala da cewa bai ji dadin abin da ya gani a wani faifan bidiyo dake nuna ana dukkan matasa da gorori tare da rungumar mata ana jefa su cikin motar Jami’an Hisba.

Jin wannan kalamai na Gwamna na Kano ne ya sa Sheikh Daurawa bayyyana murabus daga mukaminsa na babban Kwamandan Hisba, inda ya bai wa gwamna hakuri tare da rokon afuwarsa, sannan ya.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Lamarin da ake alakanta shi da fitsararriyar ‘yar TikTok Murja Kunya wadda ta shahara ta fuskar fitsara batsa da Kuma yadda wasu mazauna Unguwar Hotoro Suka yi kararta sakamakon yunkurin bata tarbiy-yar yaransu, hakan ta sa aka shelanta farautarta, wanda kuma jami’an na Hisba suka samu nasarar damke ta tare da gurfanar da ita gaban kuliya, inda daga nan alkalin kotun ya aika da ita gidan gyaran hali har zuwa lokacin da za’a dawo da ita kotu.

Amma wani abu mai kama da al’amara kawai sai aka wayi gari da jin labarin fitar da ita ba kuma tare da sanin alkalin da ya aikata Gidan Gyaran Halin ba.

Bayyana murabus din Daurawa ne ya sanya Limaman masallatan Juma’a Suka gabatar mafi yawan Hud-ubarsu kan wannan matsàla. Sai dai wasu Malamai na ta rokon Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa da dubi girman Allah ya koma bakin aikinsa. A washe garin murabus din na Daurawa wata majiyar ta Shaida wa Jaridar LEADERSHIP Hausa cewa an kwashe awa bakwai na gudanar taro kan lamarin

Babu shakka kalaman na Gwamnan Abba Kabir Yusuf ya zama abin da ko ina a Kano ke zaman abin tattaunawa, wasu na ganin barin tantiriyar ci gaba da wannan mummunar ta’adar zai kara zubarwa da Jihar Kano kimar da aka Santa dashi

Sheikh Daurawa Ya Amince Da Komawa Kan Mukaminsa

Sakamakon wani zama na musamman da wasu Malamai suka yi da Gwamnan Jihar Kano, an samu sasanci, yanzu Shaikh Aminu Daurawa zai ci gaba da shugabancin Hukumar Hisba a Kano,

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Litinin, ya bayyana cewa akwai wani zama da ya gudana tsakanin Gwamna Abba Kabir Yusuf da wata tawagar Malamai, wadanda suka hada da shi kan sa Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa bisa jago-rancin Dakta Musa Borodo da sauran Malamai irin su, Dakta Sa’idu Ahmad Dukawa, Sheikh Abdul-wahab Abdallah, Farfesa Salisu da sai sauransu.

A ta bangaren Gwamnati kuma, bisa jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, akwai mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Alhaji Jibrin Ismail Fal-gore; Sakataren Gwamnatin Jihar Kano Dakta Baffa Abdullahi Bichi, da Shugaban Ma’aikatan gidan Gwamnatin jihar, Alhaji Shehu Wada Sagagi.

Yanzu dai abin da yage shi ne sauraron jin irin salon da Kwamanda Hisbar Aminu Daurawa zai shigo da shi, shin ya gindaya wani sharadi ne kan daina yi wa ayyukan hukumar katsalandan da kokarin daurewa masu badala gindi, ko kuma an yi masa iyaka kan ayyukan na Hisba, wannan dai ta Bahaushe “Maji ma-gani, an binne tsohuwa da rai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

3 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

8 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

9 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

10 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

11 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

12 hours ago
Next Post
Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka

Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.