• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar Soji Ta Kaddamar Da Bincike Kan Zargin Da Aka Yi Wa Jami’anta Na Kashe Wani Direba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bataliyar rundunar soji ta 81 ta kaddamar da bincike dangane da zargin kisan wani direba da aka gano sunansa da Lawal da ake zargin wasu sojoji da aikatawa a jihar Legas.

 

Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a yayin da sojojin suka tsayar da shi Lawal a lokacin da ke kan hanyarsa ta kai wato sabuwar mota kirar Toyota Corolla ga mamallakinta a Abuja.

  • Rundunar Sojin Sama Ta Yi Asarar Jiragen Yaki 17 Cikin Shekara 8

An yi zargin cewan sojojin sun fada ma Lawal za su daukeshi zuwa barikinsu amma sai suka wuce da shi zuwa Iyana Ipaja da ke kan hanyar Legas inda suka harbeshi tare da yasar da gangan jikinsa a daji.

 

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Ba tare da sanin su ba, abokin Lawal wanda shi kuma yake cikin wata mota kirar Hilux ya biyo bayansa kuma ya ga dukkanin abubuwan da suka faru tare da gaggawan zuwa ya shaida wa ‘yansanda.

 

Abokin mamacin da ya kai rahoton faruwar labarin ga ‘yansandan, hakan ya bada dama aka bi sawun wadanda ake zargin a 9 Bridage, Maryland kuma an kai ga gano su ne a ranar Asabar.

 

Da ya ke maida jawabi kan wannan lamarin a yammacin ranar Lahadi, kakakin rundunar soji ta 81, Lt.-Col. Olabisi Ayeni, ya ce rundunar soji ta kaddamar da bincike kan lamarin kisan da wasu mutane sanye da kakin soja suka yi a ranar 17 ga watan Agusta.

 

Ayeni ya ce, “Tabbas mun kaddamar da bincike kuma za mu tabbatar da an yi gaskiya wajen zakulo makasan walau ko sojoji ne na gaskiya ko kuma wasu ne kawai suka yi amfani da kayan soji wajen aikata kisan.

 

“Rundunar tunin ta fara gudanar da bincike tare da hadin guiwar hukumar ‘yansanda ta jihar Legas domin tabbatar da fito da hakikanin abubuwan da suka faru kan wannan danyen aikin.

 

“A karshen binciken, idan aka gano aka tabbatar wadanda ake zargi sojoji ne, za a kawosu gaban shari’a su fuskanci hukunci na soji da na dokar farar hula.

 

“A daidai lokacin da lamarin ke kan bincike, shalkwatar soji ta 81 na rokon iyalan mamacin su kasance masu hakuri su dan jira kadan zuwa fitowar sakamakon binciken za mu kuma tabbatar musu da adalci.

 

“Rundunar soji kwata-kwata ba ta lamuntar rashin da’a daga wajen jami’anta kuma kowani mutum aka samu da aikata ta’addanci dole ne ya fuskanci hukunci.

 

“A kan hakan, Kwamandan rundunar soji ta 81, Manjo Janar MT Usman, ya jajanta wa iyalan mamacin tare da yin alkawarin sanya ido wajen wanzar da adalci yadda ya dace.

 

“Ya tabbatar wa iyalan mamacin cewa ba za a taba barin ran da uwansu ya tafi haka nan ba tare da an hukunta makasan ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Jami’in Afirka Ta Kudu Ya Gana Da Shugaban CMG

Next Post

Yunkurin Kasar Amurka Na Kafa Wata Kungiyar NATO A Yankin Asiya Da Tekun Pasific Ba Zai Yi Nasara Ba

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

5 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

8 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

9 hours ago
Soji
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

10 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

12 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

12 hours ago
Next Post
Yunkurin Kasar Amurka Na Kafa Wata Kungiyar NATO A Yankin Asiya Da Tekun Pasific Ba Zai Yi Nasara Ba

Yunkurin Kasar Amurka Na Kafa Wata Kungiyar NATO A Yankin Asiya Da Tekun Pasific Ba Zai Yi Nasara Ba

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Soji

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.