• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar Soji Ta Kaddamar Da Bincike Kan Zargin Da Aka Yi Wa Jami’anta Na Kashe Wani Direba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bataliyar rundunar soji ta 81 ta kaddamar da bincike dangane da zargin kisan wani direba da aka gano sunansa da Lawal da ake zargin wasu sojoji da aikatawa a jihar Legas.

 

Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a yayin da sojojin suka tsayar da shi Lawal a lokacin da ke kan hanyarsa ta kai wato sabuwar mota kirar Toyota Corolla ga mamallakinta a Abuja.

  • Rundunar Sojin Sama Ta Yi Asarar Jiragen Yaki 17 Cikin Shekara 8

An yi zargin cewan sojojin sun fada ma Lawal za su daukeshi zuwa barikinsu amma sai suka wuce da shi zuwa Iyana Ipaja da ke kan hanyar Legas inda suka harbeshi tare da yasar da gangan jikinsa a daji.

 

Labarai Masu Nasaba

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Ba tare da sanin su ba, abokin Lawal wanda shi kuma yake cikin wata mota kirar Hilux ya biyo bayansa kuma ya ga dukkanin abubuwan da suka faru tare da gaggawan zuwa ya shaida wa ‘yansanda.

 

Abokin mamacin da ya kai rahoton faruwar labarin ga ‘yansandan, hakan ya bada dama aka bi sawun wadanda ake zargin a 9 Bridage, Maryland kuma an kai ga gano su ne a ranar Asabar.

 

Da ya ke maida jawabi kan wannan lamarin a yammacin ranar Lahadi, kakakin rundunar soji ta 81, Lt.-Col. Olabisi Ayeni, ya ce rundunar soji ta kaddamar da bincike kan lamarin kisan da wasu mutane sanye da kakin soja suka yi a ranar 17 ga watan Agusta.

 

Ayeni ya ce, “Tabbas mun kaddamar da bincike kuma za mu tabbatar da an yi gaskiya wajen zakulo makasan walau ko sojoji ne na gaskiya ko kuma wasu ne kawai suka yi amfani da kayan soji wajen aikata kisan.

 

“Rundunar tunin ta fara gudanar da bincike tare da hadin guiwar hukumar ‘yansanda ta jihar Legas domin tabbatar da fito da hakikanin abubuwan da suka faru kan wannan danyen aikin.

 

“A karshen binciken, idan aka gano aka tabbatar wadanda ake zargi sojoji ne, za a kawosu gaban shari’a su fuskanci hukunci na soji da na dokar farar hula.

 

“A daidai lokacin da lamarin ke kan bincike, shalkwatar soji ta 81 na rokon iyalan mamacin su kasance masu hakuri su dan jira kadan zuwa fitowar sakamakon binciken za mu kuma tabbatar musu da adalci.

 

“Rundunar soji kwata-kwata ba ta lamuntar rashin da’a daga wajen jami’anta kuma kowani mutum aka samu da aikata ta’addanci dole ne ya fuskanci hukunci.

 

“A kan hakan, Kwamandan rundunar soji ta 81, Manjo Janar MT Usman, ya jajanta wa iyalan mamacin tare da yin alkawarin sanya ido wajen wanzar da adalci yadda ya dace.

 

“Ya tabbatar wa iyalan mamacin cewa ba za a taba barin ran da uwansu ya tafi haka nan ba tare da an hukunta makasan ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Jami’in Afirka Ta Kudu Ya Gana Da Shugaban CMG

Next Post

Yunkurin Kasar Amurka Na Kafa Wata Kungiyar NATO A Yankin Asiya Da Tekun Pasific Ba Zai Yi Nasara Ba

Related

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

3 hours ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

4 hours ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

6 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

7 hours ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

7 hours ago
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
Labarai

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

8 hours ago
Next Post
Yunkurin Kasar Amurka Na Kafa Wata Kungiyar NATO A Yankin Asiya Da Tekun Pasific Ba Zai Yi Nasara Ba

Yunkurin Kasar Amurka Na Kafa Wata Kungiyar NATO A Yankin Asiya Da Tekun Pasific Ba Zai Yi Nasara Ba

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.