ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar Soji Ta Kaddamar Da Bincike Kan Zargin Da Aka Yi Wa Jami’anta Na Kashe Wani Direba

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Soji

Bataliyar rundunar soji ta 81 ta kaddamar da bincike dangane da zargin kisan wani direba da aka gano sunansa da Lawal da ake zargin wasu sojoji da aikatawa a jihar Legas.

 

Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a yayin da sojojin suka tsayar da shi Lawal a lokacin da ke kan hanyarsa ta kai wato sabuwar mota kirar Toyota Corolla ga mamallakinta a Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Rundunar Sojin Sama Ta Yi Asarar Jiragen Yaki 17 Cikin Shekara 8

An yi zargin cewan sojojin sun fada ma Lawal za su daukeshi zuwa barikinsu amma sai suka wuce da shi zuwa Iyana Ipaja da ke kan hanyar Legas inda suka harbeshi tare da yasar da gangan jikinsa a daji.

 

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Ba tare da sanin su ba, abokin Lawal wanda shi kuma yake cikin wata mota kirar Hilux ya biyo bayansa kuma ya ga dukkanin abubuwan da suka faru tare da gaggawan zuwa ya shaida wa ‘yansanda.

 

Abokin mamacin da ya kai rahoton faruwar labarin ga ‘yansandan, hakan ya bada dama aka bi sawun wadanda ake zargin a 9 Bridage, Maryland kuma an kai ga gano su ne a ranar Asabar.

 

Da ya ke maida jawabi kan wannan lamarin a yammacin ranar Lahadi, kakakin rundunar soji ta 81, Lt.-Col. Olabisi Ayeni, ya ce rundunar soji ta kaddamar da bincike kan lamarin kisan da wasu mutane sanye da kakin soja suka yi a ranar 17 ga watan Agusta.

 

Ayeni ya ce, “Tabbas mun kaddamar da bincike kuma za mu tabbatar da an yi gaskiya wajen zakulo makasan walau ko sojoji ne na gaskiya ko kuma wasu ne kawai suka yi amfani da kayan soji wajen aikata kisan.

 

“Rundunar tunin ta fara gudanar da bincike tare da hadin guiwar hukumar ‘yansanda ta jihar Legas domin tabbatar da fito da hakikanin abubuwan da suka faru kan wannan danyen aikin.

 

“A karshen binciken, idan aka gano aka tabbatar wadanda ake zargi sojoji ne, za a kawosu gaban shari’a su fuskanci hukunci na soji da na dokar farar hula.

 

“A daidai lokacin da lamarin ke kan bincike, shalkwatar soji ta 81 na rokon iyalan mamacin su kasance masu hakuri su dan jira kadan zuwa fitowar sakamakon binciken za mu kuma tabbatar musu da adalci.

 

“Rundunar soji kwata-kwata ba ta lamuntar rashin da’a daga wajen jami’anta kuma kowani mutum aka samu da aikata ta’addanci dole ne ya fuskanci hukunci.

 

“A kan hakan, Kwamandan rundunar soji ta 81, Manjo Janar MT Usman, ya jajanta wa iyalan mamacin tare da yin alkawarin sanya ido wajen wanzar da adalci yadda ya dace.

 

“Ya tabbatar wa iyalan mamacin cewa ba za a taba barin ran da uwansu ya tafi haka nan ba tare da an hukunta makasan ba.”

Soji
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Yunkurin Kasar Amurka Na Kafa Wata Kungiyar NATO A Yankin Asiya Da Tekun Pasific Ba Zai Yi Nasara Ba

Yunkurin Kasar Amurka Na Kafa Wata Kungiyar NATO A Yankin Asiya Da Tekun Pasific Ba Zai Yi Nasara Ba

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.