ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar Soji Ta Kaddamar Da Bincike Kan Zargin Da Aka Yi Wa Jami’anta Na Kashe Wani Direba

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Soji

Bataliyar rundunar soji ta 81 ta kaddamar da bincike dangane da zargin kisan wani direba da aka gano sunansa da Lawal da ake zargin wasu sojoji da aikatawa a jihar Legas.

 

Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a yayin da sojojin suka tsayar da shi Lawal a lokacin da ke kan hanyarsa ta kai wato sabuwar mota kirar Toyota Corolla ga mamallakinta a Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Rundunar Sojin Sama Ta Yi Asarar Jiragen Yaki 17 Cikin Shekara 8

An yi zargin cewan sojojin sun fada ma Lawal za su daukeshi zuwa barikinsu amma sai suka wuce da shi zuwa Iyana Ipaja da ke kan hanyar Legas inda suka harbeshi tare da yasar da gangan jikinsa a daji.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ba tare da sanin su ba, abokin Lawal wanda shi kuma yake cikin wata mota kirar Hilux ya biyo bayansa kuma ya ga dukkanin abubuwan da suka faru tare da gaggawan zuwa ya shaida wa ‘yansanda.

 

Abokin mamacin da ya kai rahoton faruwar labarin ga ‘yansandan, hakan ya bada dama aka bi sawun wadanda ake zargin a 9 Bridage, Maryland kuma an kai ga gano su ne a ranar Asabar.

 

Da ya ke maida jawabi kan wannan lamarin a yammacin ranar Lahadi, kakakin rundunar soji ta 81, Lt.-Col. Olabisi Ayeni, ya ce rundunar soji ta kaddamar da bincike kan lamarin kisan da wasu mutane sanye da kakin soja suka yi a ranar 17 ga watan Agusta.

 

Ayeni ya ce, “Tabbas mun kaddamar da bincike kuma za mu tabbatar da an yi gaskiya wajen zakulo makasan walau ko sojoji ne na gaskiya ko kuma wasu ne kawai suka yi amfani da kayan soji wajen aikata kisan.

 

“Rundunar tunin ta fara gudanar da bincike tare da hadin guiwar hukumar ‘yansanda ta jihar Legas domin tabbatar da fito da hakikanin abubuwan da suka faru kan wannan danyen aikin.

 

“A karshen binciken, idan aka gano aka tabbatar wadanda ake zargi sojoji ne, za a kawosu gaban shari’a su fuskanci hukunci na soji da na dokar farar hula.

 

“A daidai lokacin da lamarin ke kan bincike, shalkwatar soji ta 81 na rokon iyalan mamacin su kasance masu hakuri su dan jira kadan zuwa fitowar sakamakon binciken za mu kuma tabbatar musu da adalci.

 

“Rundunar soji kwata-kwata ba ta lamuntar rashin da’a daga wajen jami’anta kuma kowani mutum aka samu da aikata ta’addanci dole ne ya fuskanci hukunci.

 

“A kan hakan, Kwamandan rundunar soji ta 81, Manjo Janar MT Usman, ya jajanta wa iyalan mamacin tare da yin alkawarin sanya ido wajen wanzar da adalci yadda ya dace.

 

“Ya tabbatar wa iyalan mamacin cewa ba za a taba barin ran da uwansu ya tafi haka nan ba tare da an hukunta makasan ba.”

Soji
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Yunkurin Kasar Amurka Na Kafa Wata Kungiyar NATO A Yankin Asiya Da Tekun Pasific Ba Zai Yi Nasara Ba

Yunkurin Kasar Amurka Na Kafa Wata Kungiyar NATO A Yankin Asiya Da Tekun Pasific Ba Zai Yi Nasara Ba

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.