• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rusau: ‘Yan Kasuwar Kano 5,000 Za Su Rasa Shagunansu Bayan Shafe Shekaru 18 A Kasuwa

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
in Labarai
0
Rusau: ‘Yan Kasuwar Kano 5,000 Za Su Rasa Shagunansu Bayan Shafe Shekaru 18 A Kasuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙalla ƴan kasuwa 5,000 ne za su rasa shagunansu waɗanda ke kasuwanci a kusa da babban masallacin Idi na Kano, biyo bayan sanarwar da hukumar tsare-tsare da raya birane ta jihar Kano, KNUPDA ta yi musu.

Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa, Shugaban ƙungiyar ƴan kasuwar, Yakubu Muhammad, ne ya bayyana haka a ranar Talata yayin wata ganawa da manema labarai.

  • Kansila Ya Ɗauki Nauyin Karatun Ɗalibai 120 A Kano
  • Boko Haram Sun Sace Fasinjoji A Kan Hanyar Maiduguri Zuwa Kano

Hukumar KNUPDA ta bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga ‘yan kasuwa a masallacin da ke kan titin IBB a cikin birnin Kano da su bar gurin ko kuma su fuskanci fushin doka.

Malam Muhammad ya bayyana cewa shekaru 18 da suka gabata Marigayi Galadima na Kano, Tijjani Hashim ne ya raba musu wurin ta hannun Masarautar Kano.

“An ware wurin ne ga mambobinmu domin duba ayyukan laifuka daban-daban kamar satar waya da sauran ayyukan ɓata gari da ake tafkawa a wuraren,” inji shi.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Ya ce gwamnatocin da suka gabata a jihar sun ga ya dace a bar ‘yan kasuwar su ci gaba da gudanar da ayyukansu a yankin.

“Muna da yawa a nan, galibi matasa ne, ta yaya za ku yi ƙoƙarin raba waɗannan mutane da kasuwancinsu, kun san hakan zai haifar da haɗari ga jihar,” in ji shi.

Malam Muhammad ya ce, “Har yanzu muna ƙoƙarin ganin mun shawo kan haƙiƙanin laifin da muka aikata wanda ya sa KNUPDA zata fatattake mu daga inda muke gudanar da sana’o’inmu na halal ba domin kula da iyalanmu.

“Mun goyi bayan wannan gwamnati. Mun zabe shi a lokacin zaben 2023. Mafi kyawun sakayyar da wannan gwamnati za ta yi mana bai wuce ta ba mu damar ci gaba da kasuwancinmu a Masallacin Idi,” in ji shi.

Da aka tuntubi wata majiya a KNUPDA da ta nemi a sakaya sunanta ta tabbatar da cewa hukumar ta umurci ‘yan kasuwar da su bar wurin saboda sun mamaye wurin ne ba bisa ka’ida ba.

“KNUPDA na ganin ‘yan kasuwar ba su nemi izini daga gare ta ba kafin su fara kasuwanci a can.” Inji majiyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoKasuwaKnupaMasallacin IdiTrade
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kara Mu’amala Tsakanin Mabambantan Al’ummomin Duniya Zai Kawar Da Sabani Da Rashin Fahimta

Next Post

Shugaban CMG Ya Aike Da Wasika Ga Wata Ba’amurkiya Abokiyar Sinawa

Related

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

7 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

9 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

12 hours ago
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

13 hours ago
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
Labarai

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

14 hours ago
DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

16 hours ago
Next Post
Shugaban CMG Ya Aike Da Wasika Ga Wata Ba’amurkiya Abokiyar Sinawa

Shugaban CMG Ya Aike Da Wasika Ga Wata Ba’amurkiya Abokiyar Sinawa

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.