• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rusau: ‘Yan Kasuwar Kano 5,000 Za Su Rasa Shagunansu Bayan Shafe Shekaru 18 A Kasuwa

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Rusau: ‘Yan Kasuwar Kano 5,000 Za Su Rasa Shagunansu Bayan Shafe Shekaru 18 A Kasuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙalla ƴan kasuwa 5,000 ne za su rasa shagunansu waɗanda ke kasuwanci a kusa da babban masallacin Idi na Kano, biyo bayan sanarwar da hukumar tsare-tsare da raya birane ta jihar Kano, KNUPDA ta yi musu.

Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa, Shugaban ƙungiyar ƴan kasuwar, Yakubu Muhammad, ne ya bayyana haka a ranar Talata yayin wata ganawa da manema labarai.

  • Kansila Ya Ɗauki Nauyin Karatun Ɗalibai 120 A Kano
  • Boko Haram Sun Sace Fasinjoji A Kan Hanyar Maiduguri Zuwa Kano

Hukumar KNUPDA ta bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga ‘yan kasuwa a masallacin da ke kan titin IBB a cikin birnin Kano da su bar gurin ko kuma su fuskanci fushin doka.

Malam Muhammad ya bayyana cewa shekaru 18 da suka gabata Marigayi Galadima na Kano, Tijjani Hashim ne ya raba musu wurin ta hannun Masarautar Kano.

“An ware wurin ne ga mambobinmu domin duba ayyukan laifuka daban-daban kamar satar waya da sauran ayyukan ɓata gari da ake tafkawa a wuraren,” inji shi.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ya ce gwamnatocin da suka gabata a jihar sun ga ya dace a bar ‘yan kasuwar su ci gaba da gudanar da ayyukansu a yankin.

“Muna da yawa a nan, galibi matasa ne, ta yaya za ku yi ƙoƙarin raba waɗannan mutane da kasuwancinsu, kun san hakan zai haifar da haɗari ga jihar,” in ji shi.

Malam Muhammad ya ce, “Har yanzu muna ƙoƙarin ganin mun shawo kan haƙiƙanin laifin da muka aikata wanda ya sa KNUPDA zata fatattake mu daga inda muke gudanar da sana’o’inmu na halal ba domin kula da iyalanmu.

“Mun goyi bayan wannan gwamnati. Mun zabe shi a lokacin zaben 2023. Mafi kyawun sakayyar da wannan gwamnati za ta yi mana bai wuce ta ba mu damar ci gaba da kasuwancinmu a Masallacin Idi,” in ji shi.

Da aka tuntubi wata majiya a KNUPDA da ta nemi a sakaya sunanta ta tabbatar da cewa hukumar ta umurci ‘yan kasuwar da su bar wurin saboda sun mamaye wurin ne ba bisa ka’ida ba.

“KNUPDA na ganin ‘yan kasuwar ba su nemi izini daga gare ta ba kafin su fara kasuwanci a can.” Inji majiyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoKasuwaKnupaMasallacin IdiTrade
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kara Mu’amala Tsakanin Mabambantan Al’ummomin Duniya Zai Kawar Da Sabani Da Rashin Fahimta

Next Post

Shugaban CMG Ya Aike Da Wasika Ga Wata Ba’amurkiya Abokiyar Sinawa

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

3 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

4 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

4 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

5 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

7 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

8 hours ago
Next Post
Shugaban CMG Ya Aike Da Wasika Ga Wata Ba’amurkiya Abokiyar Sinawa

Shugaban CMG Ya Aike Da Wasika Ga Wata Ba’amurkiya Abokiyar Sinawa

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.