• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rushe Daula: Kamfani Ya Garzaya Kotu, Kan Gwamnatin Kano Ta Biya Shi Diyyar ₦ 10bn

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rushe Daula: Kamfani Ya Garzaya Kotu, Kan Gwamnatin Kano Ta Biya Shi Diyyar ₦ 10bn
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani kamfani mai zaman kansa, Lamash Property Limited, wanda ya kulla huldar kasuwanci da gwamnatin jihar Kano kan sake gina Otel din Daula, ya bukaci a biya shi diyyar Naira biliyan 10 biyo bayan rushe wurin da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi a ranar Asabar.

Kazalika, wani kamfani mai suna White Nig. Ltd wanda shi ma suka kulla yarjejeniya kan tsarin PPP tare da gwamnatin jihar Kano don bunkasa sansanin Hajjin bana a jihar, ya ce abin ya ba shi mamaki da abin da ya kira matakin farko na sabuwar gwamnatin jihar.

  • Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano
  • Abba Gida-Gida Ya Ba Da Umarnin Rushe Gine-Ginen Da Aka Yi A Filayen Gwamnati

Manajin Darakta na kamfanin, Hassan Yusuf Baba, ya ce: “Abin takaicin shi ne mu
ba a sanar da mu ba, mun tashi ne kawai muka ga a kafafen sada zumunta cewa an ruguje dukkan gine-gine. Wannan zalunci ne babba wanda ba za mu nade hannunmu mu ga abin ya faru a jiharmu ba, mun kammala duk wani shiri na garzaya wa kotu domin neman hakkinmu.

Wani mai suna Dan Asabe Abubakar, wanda aka rusa gininsa gabanin ruguje Otal din Daula da kuma Hajj Camp, wanda ya gina rukunin shaguna na Filin Sukuwar Dawaki da ke dauke da dakin motsa jiki, dakin gwaje-gwaje na likitoci, da sauran muhimman sassa, ya koka. yadda ya kashe sama da Naira biliyan 1.4 kan aikin.

Ya fusata kan yadda gwamnatin jihar ke rusa kadarorin jama’a ba tare da bin dokar amfani da filaye ba.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

Lamash Property Limited, a cikin wata sanarwa mai suna, ‘GOVERNMENT DEMOLITION OF DAULA HOTEL: OUR STAND’, wacce hukumar gudanarwar ta sa hannun a ranar Lahadi, ta ce za ta shigar da kara Kotu suna masu neman diyyar Naira biliyan 10, wanda shi ne kudin da aka riga aka kashe a aikin.

Kamfanin wanda ya bayyana mamakin yadda sabuwar gwamnatin Kano za ta iya kaiwa ga ruguza wani otel na biliyoyin nairori mallakin ta da ko wace fuska, ta ce an fara aikin ne a karkashin gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje, kan tsarin yarjejeniyar PPP. don samar da ayyukan yi ga jama’a da samar da kudaden shiga ga jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Gida-gidakanoKotuRushe Daula
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Yi Gargadi Game Da Yadda Wasu Ke Neman Gurgunta Yanayin Tsaro A yankin Asiya Da Tekun Pasific

Next Post

Benzema Ya Bar Real Madrid Bayan Shekaru 14 A Kungiyar

Related

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

13 hours ago
Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

14 hours ago
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

20 hours ago
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

23 hours ago
Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

2 days ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

2 days ago
Next Post
Benzema Ya Bar Real Madrid Bayan Shekaru 14 A Kungiyar

Benzema Ya Bar Real Madrid Bayan Shekaru 14 A Kungiyar

LABARAI MASU NASABA

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

July 31, 2025
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

July 31, 2025
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

July 31, 2025
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.