• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rushe Daula: Kamfani Ya Garzaya Kotu, Kan Gwamnatin Kano Ta Biya Shi Diyyar ₦ 10bn

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rushe Daula: Kamfani Ya Garzaya Kotu, Kan Gwamnatin Kano Ta Biya Shi Diyyar ₦ 10bn
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani kamfani mai zaman kansa, Lamash Property Limited, wanda ya kulla huldar kasuwanci da gwamnatin jihar Kano kan sake gina Otel din Daula, ya bukaci a biya shi diyyar Naira biliyan 10 biyo bayan rushe wurin da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi a ranar Asabar.

Kazalika, wani kamfani mai suna White Nig. Ltd wanda shi ma suka kulla yarjejeniya kan tsarin PPP tare da gwamnatin jihar Kano don bunkasa sansanin Hajjin bana a jihar, ya ce abin ya ba shi mamaki da abin da ya kira matakin farko na sabuwar gwamnatin jihar.

  • Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano
  • Abba Gida-Gida Ya Ba Da Umarnin Rushe Gine-Ginen Da Aka Yi A Filayen Gwamnati

Manajin Darakta na kamfanin, Hassan Yusuf Baba, ya ce: “Abin takaicin shi ne mu
ba a sanar da mu ba, mun tashi ne kawai muka ga a kafafen sada zumunta cewa an ruguje dukkan gine-gine. Wannan zalunci ne babba wanda ba za mu nade hannunmu mu ga abin ya faru a jiharmu ba, mun kammala duk wani shiri na garzaya wa kotu domin neman hakkinmu.

Wani mai suna Dan Asabe Abubakar, wanda aka rusa gininsa gabanin ruguje Otal din Daula da kuma Hajj Camp, wanda ya gina rukunin shaguna na Filin Sukuwar Dawaki da ke dauke da dakin motsa jiki, dakin gwaje-gwaje na likitoci, da sauran muhimman sassa, ya koka. yadda ya kashe sama da Naira biliyan 1.4 kan aikin.

Ya fusata kan yadda gwamnatin jihar ke rusa kadarorin jama’a ba tare da bin dokar amfani da filaye ba.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

Lamash Property Limited, a cikin wata sanarwa mai suna, ‘GOVERNMENT DEMOLITION OF DAULA HOTEL: OUR STAND’, wacce hukumar gudanarwar ta sa hannun a ranar Lahadi, ta ce za ta shigar da kara Kotu suna masu neman diyyar Naira biliyan 10, wanda shi ne kudin da aka riga aka kashe a aikin.

Kamfanin wanda ya bayyana mamakin yadda sabuwar gwamnatin Kano za ta iya kaiwa ga ruguza wani otel na biliyoyin nairori mallakin ta da ko wace fuska, ta ce an fara aikin ne a karkashin gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje, kan tsarin yarjejeniyar PPP. don samar da ayyukan yi ga jama’a da samar da kudaden shiga ga jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Gida-gidakanoKotuRushe Daula
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Yi Gargadi Game Da Yadda Wasu Ke Neman Gurgunta Yanayin Tsaro A yankin Asiya Da Tekun Pasific

Next Post

Benzema Ya Bar Real Madrid Bayan Shekaru 14 A Kungiyar

Related

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

49 minutes ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

20 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

1 day ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

1 day ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

2 days ago
Next Post
Benzema Ya Bar Real Madrid Bayan Shekaru 14 A Kungiyar

Benzema Ya Bar Real Madrid Bayan Shekaru 14 A Kungiyar

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.