• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rushe Daula: Kamfani Ya Garzaya Kotu, Kan Gwamnatin Kano Ta Biya Shi Diyyar ₦ 10bn

by Muhammad
2 years ago
Rushe Daula

Wani kamfani mai zaman kansa, Lamash Property Limited, wanda ya kulla huldar kasuwanci da gwamnatin jihar Kano kan sake gina Otel din Daula, ya bukaci a biya shi diyyar Naira biliyan 10 biyo bayan rushe wurin da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi a ranar Asabar.

Kazalika, wani kamfani mai suna White Nig. Ltd wanda shi ma suka kulla yarjejeniya kan tsarin PPP tare da gwamnatin jihar Kano don bunkasa sansanin Hajjin bana a jihar, ya ce abin ya ba shi mamaki da abin da ya kira matakin farko na sabuwar gwamnatin jihar.

  • Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano
  • Abba Gida-Gida Ya Ba Da Umarnin Rushe Gine-Ginen Da Aka Yi A Filayen Gwamnati

Manajin Darakta na kamfanin, Hassan Yusuf Baba, ya ce: “Abin takaicin shi ne mu
ba a sanar da mu ba, mun tashi ne kawai muka ga a kafafen sada zumunta cewa an ruguje dukkan gine-gine. Wannan zalunci ne babba wanda ba za mu nade hannunmu mu ga abin ya faru a jiharmu ba, mun kammala duk wani shiri na garzaya wa kotu domin neman hakkinmu.

Wani mai suna Dan Asabe Abubakar, wanda aka rusa gininsa gabanin ruguje Otal din Daula da kuma Hajj Camp, wanda ya gina rukunin shaguna na Filin Sukuwar Dawaki da ke dauke da dakin motsa jiki, dakin gwaje-gwaje na likitoci, da sauran muhimman sassa, ya koka. yadda ya kashe sama da Naira biliyan 1.4 kan aikin.

Ya fusata kan yadda gwamnatin jihar ke rusa kadarorin jama’a ba tare da bin dokar amfani da filaye ba.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Lamash Property Limited, a cikin wata sanarwa mai suna, ‘GOVERNMENT DEMOLITION OF DAULA HOTEL: OUR STAND’, wacce hukumar gudanarwar ta sa hannun a ranar Lahadi, ta ce za ta shigar da kara Kotu suna masu neman diyyar Naira biliyan 10, wanda shi ne kudin da aka riga aka kashe a aikin.

Kamfanin wanda ya bayyana mamakin yadda sabuwar gwamnatin Kano za ta iya kaiwa ga ruguza wani otel na biliyoyin nairori mallakin ta da ko wace fuska, ta ce an fara aikin ne a karkashin gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje, kan tsarin yarjejeniyar PPP. don samar da ayyukan yi ga jama’a da samar da kudaden shiga ga jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Next Post
Benzema Ya Bar Real Madrid Bayan Shekaru 14 A Kungiyar

Benzema Ya Bar Real Madrid Bayan Shekaru 14 A Kungiyar

LABARAI MASU NASABA

peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.