• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rushe Daula: Kamfani Ya Garzaya Kotu, Kan Gwamnatin Kano Ta Biya Shi Diyyar ₦ 10bn

by Muhammad
2 years ago
Rushe Daula

Wani kamfani mai zaman kansa, Lamash Property Limited, wanda ya kulla huldar kasuwanci da gwamnatin jihar Kano kan sake gina Otel din Daula, ya bukaci a biya shi diyyar Naira biliyan 10 biyo bayan rushe wurin da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi a ranar Asabar.

Kazalika, wani kamfani mai suna White Nig. Ltd wanda shi ma suka kulla yarjejeniya kan tsarin PPP tare da gwamnatin jihar Kano don bunkasa sansanin Hajjin bana a jihar, ya ce abin ya ba shi mamaki da abin da ya kira matakin farko na sabuwar gwamnatin jihar.

  • Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano
  • Abba Gida-Gida Ya Ba Da Umarnin Rushe Gine-Ginen Da Aka Yi A Filayen Gwamnati

Manajin Darakta na kamfanin, Hassan Yusuf Baba, ya ce: “Abin takaicin shi ne mu
ba a sanar da mu ba, mun tashi ne kawai muka ga a kafafen sada zumunta cewa an ruguje dukkan gine-gine. Wannan zalunci ne babba wanda ba za mu nade hannunmu mu ga abin ya faru a jiharmu ba, mun kammala duk wani shiri na garzaya wa kotu domin neman hakkinmu.

Wani mai suna Dan Asabe Abubakar, wanda aka rusa gininsa gabanin ruguje Otal din Daula da kuma Hajj Camp, wanda ya gina rukunin shaguna na Filin Sukuwar Dawaki da ke dauke da dakin motsa jiki, dakin gwaje-gwaje na likitoci, da sauran muhimman sassa, ya koka. yadda ya kashe sama da Naira biliyan 1.4 kan aikin.

Ya fusata kan yadda gwamnatin jihar ke rusa kadarorin jama’a ba tare da bin dokar amfani da filaye ba.

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

Lamash Property Limited, a cikin wata sanarwa mai suna, ‘GOVERNMENT DEMOLITION OF DAULA HOTEL: OUR STAND’, wacce hukumar gudanarwar ta sa hannun a ranar Lahadi, ta ce za ta shigar da kara Kotu suna masu neman diyyar Naira biliyan 10, wanda shi ne kudin da aka riga aka kashe a aikin.

Kamfanin wanda ya bayyana mamakin yadda sabuwar gwamnatin Kano za ta iya kaiwa ga ruguza wani otel na biliyoyin nairori mallakin ta da ko wace fuska, ta ce an fara aikin ne a karkashin gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje, kan tsarin yarjejeniyar PPP. don samar da ayyukan yi ga jama’a da samar da kudaden shiga ga jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya
Manyan Labarai

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Next Post
Benzema Ya Bar Real Madrid Bayan Shekaru 14 A Kungiyar

Benzema Ya Bar Real Madrid Bayan Shekaru 14 A Kungiyar

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.