• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Shirin Kasar Sin Zai Taimakawa Raya Masana’antu A Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Ra'ayi Riga
0
Sabon Shirin Kasar Sin Zai Taimakawa Raya Masana’antu A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wajen wani taron da shugabannin kasar Sin suka kira a kwanan baya, dangane da aikin raya tattalin arziki, an jaddada muhimmancin manufar raya sabon karfin samar da bunkasuwa. Makasudin wannan manufa shi ne sa kaimi ga kokarin kirkiro sabbin fasahohi, daga baya a yi amfani da fasahohin da aka samar wajen raya masana’antu. Kana manufar ta kunshi fannonin da suka hada da inganta tsoffin masana’antu ta hanyar fasahar zamani, da raya sabon makamashi, da harkar sadarwa, da sauran sabbin ayyukan masana’antu. Gami da raya masana’antun da za su samar da amfani a nan gaba, kamar masu alaka da na’ura mai kwakwalwa ta kwamfuta irin na Quantum, da fasahar sadarwa ta 6G, da dai sauransu, da kuma horar da kwararrun ma’aikata da za su iya sarrafa sabbin fasahohi.

A ganina, wannan manufa ta kasar Sin za ta samar da dama mai muhimmanci ta raya masana’antu a nahiyar Afirka.

  • Shugaban Kasar Saliyo Zai Kawo Ziyara A Kasar Sin
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 3 Kan Zargin Tayar Da Hargitsi A Kasuwar ‘Yan Magani Ta Kano

To, ko me ya sa nake iya tabbatar da haka? Saboda da farko, kasar Sin mai goyon bayan kasashen Afirka ce a fannin raya masana’antu.

Kasar Sin ta kwashe shekaru fiye da 100 tana kokarin raya bangaren masana’antunta, inda ta sha wahalhalu da matsin lamba iri daya da wadanda kasashen Afirka ke fama da su. Kana bisa kokarin nema, kasar ta samu dabarar bunkasa masana’antu mai dacewa. Saboda haka, dangane da mawuyacin halin da kasashe masu raunin tattalin arziki suke ciki ta fuskar raya masana’antu, kasar Sin tana da wani ra’ayi da ya sha bamban da na kasashen yamma, inda kasar Sin ta kan jaddada muhimmancin raya tattalin arziki da inganta bangaren masana’antu a kasashe masu tasowa. Kana yayin da kasar ke neman raya masana’antunta, tana kuma fatan ganin kasashen Afirka sun samu ci gaba na bai daya, da kawo karshen yanayin koma bayan tattalin arziki, da sarrafawa da cin zarafi da kasashen yamma ke yi musu.

Na biyu shi ne, sabanin yadda kasashen yamma ke kallon tsarinsu a matsayin wanda ya fi kyau a duniya, da yadda suke son ba da umarni ga kasashen Afirka, kasar Sin ta kan samar da dabarar raya masana’antu da ta dace da hakikanin yanayin da kasashen Afirka suke ciki.

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Misali, ta la’akari da yadda ake fama da karancin tsare-tsaren da za su taimakawa raya masana’antu, da rashin isassun hanyoyin jigilar kayayyaki a Afirka, kasar Sin ta dauki wasu matakai 3 yayin da take aiwatar da ayyukan hadin gwiwa na raya masana’antu a kasashen Afirka: Da farko ta gina dimbin yankunan masana’antu don tabbatar da gudanar ayyukan manyan ma’aikatu yadda ake bukata. Kana na biyu shi ne, kasar Sin da kasashen Afirka sun kirkiro ayyukan masana’antu masu alaka da kayayyakin more rayuwa da aka gina, don tabbatar da cewa kudin da aka kashe wajen gina kayayyakin more rayuwa na samar da amfani da riba. Yayin da na 3 shi ne, kasar Sin na dora muhimmanci kan zuba jari ga masana’antun samar da kayayyakin da ake bukatarsu a kasuwannin kasashen Afirka, lamarin da ya ingiza tsarin raya masana’antu na kasashen Afirka na mai da hankali kan kasuwannin cikin gida, ta yadda ake tabbatar da ci gaban aikin raya bangaren masana’antu a kai a kai.

Ban da haka, dalili na karshe da ya sa nake sa ran ganin amfanin manufar kasar Sin kan raya masana’antu a Afirka shi ne, kasar ta dade tana samar da fasahohin samun ci gaba ga kasashen Afirka, don ciyar da tattalin arzikinsu gaba ta wata ingatacciyar hanya.

Misali, a shekarun baya, karin kasashen dake nahiyar Afirka sun mai da tattalin arziki mai alaka da fasahohin zamani a matsayin sabuwar dabarar neman samun ci gaba, bisa hadin gwiwa da kasar Sin. A kasashen da suka hada da Najeriya da Kenya, da dai sauransu, dandalin biyan kudi ta wayar salula da kamfanoni masu jarin kasar Sin suka kafa na samar da dabarar biyan kudi mai tsaro da sauki ga mutane fiye da miliyan 10. A sa’i daya, kamfanonin kasar Sin sun kaddamar da ayyukan horar da kwararru na fannonin fasahar sadarwa, da ciniki ta yanar gizo ko Internet a kasashen Afirka, inda aka ba dimbin matasan nahiyar Afirka damammaki na koyon fasahohi masu inganci, da wadanda suka shafi kafawa da kula da kamfanoni, ta yadda za a taimakawa kasashen Afirka a fannin zamanantar da fasahohi.

Ta wadannan abubuwa da na bayyana za mu san cewa, kasar Sin na son taimakon kasashen Afirka wajen raya masana’antu, kuma ta san dabara mai dacewa da ya kamata a dauka don taimakawa. Ban da haka, kasar ta dade tana raba fasahohinta masu inganci ga kasashen Afirka, don neman samun ci gaban tattalin arzikinsu na bai daya. Saboda haka, kokarin kasar Sin na raya sabbin fasahohi da sabbin nau’ikan masana’antu tabbas zai samar da damammaki masu kyau na raya tattalin arziki ga kasashen Afirka.

Na kan ji yadda abokaina na Najeriya suke fadin cewa, “A lokacin da kasar Sin ta hau duniyar wata, to, ta tafi tare da Najeriya. ” To, idan kun yarda, zan so in gyara maganar, sa’an nan in sanya ta a karshen wannan sharhi, wato: Lokacin da Sin ta hau duniyar wata, tabbas za a samu kasashen Afirka a can, tare da kasar Sin. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Zamfara Ta Dakatar Da Mambobi 8 Tare Da Rusa Kwamitocinta

Next Post

Gobara Ta Kone Shaguna 50 A Kasuwar ‘Yan Katako A Kano

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

4 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

1 week ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

1 week ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

1 week ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

1 week ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 weeks ago
Next Post
Hukumar kashe gobara

Gobara Ta Kone Shaguna 50 A Kasuwar 'Yan Katako A Kano

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.