• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Shirin Kasar Sin Zai Taimakawa Raya Masana’antu A Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Ra'ayi Riga
0
Sabon Shirin Kasar Sin Zai Taimakawa Raya Masana’antu A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wajen wani taron da shugabannin kasar Sin suka kira a kwanan baya, dangane da aikin raya tattalin arziki, an jaddada muhimmancin manufar raya sabon karfin samar da bunkasuwa. Makasudin wannan manufa shi ne sa kaimi ga kokarin kirkiro sabbin fasahohi, daga baya a yi amfani da fasahohin da aka samar wajen raya masana’antu. Kana manufar ta kunshi fannonin da suka hada da inganta tsoffin masana’antu ta hanyar fasahar zamani, da raya sabon makamashi, da harkar sadarwa, da sauran sabbin ayyukan masana’antu. Gami da raya masana’antun da za su samar da amfani a nan gaba, kamar masu alaka da na’ura mai kwakwalwa ta kwamfuta irin na Quantum, da fasahar sadarwa ta 6G, da dai sauransu, da kuma horar da kwararrun ma’aikata da za su iya sarrafa sabbin fasahohi.

A ganina, wannan manufa ta kasar Sin za ta samar da dama mai muhimmanci ta raya masana’antu a nahiyar Afirka.

  • Shugaban Kasar Saliyo Zai Kawo Ziyara A Kasar Sin
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 3 Kan Zargin Tayar Da Hargitsi A Kasuwar ‘Yan Magani Ta Kano

To, ko me ya sa nake iya tabbatar da haka? Saboda da farko, kasar Sin mai goyon bayan kasashen Afirka ce a fannin raya masana’antu.

Kasar Sin ta kwashe shekaru fiye da 100 tana kokarin raya bangaren masana’antunta, inda ta sha wahalhalu da matsin lamba iri daya da wadanda kasashen Afirka ke fama da su. Kana bisa kokarin nema, kasar ta samu dabarar bunkasa masana’antu mai dacewa. Saboda haka, dangane da mawuyacin halin da kasashe masu raunin tattalin arziki suke ciki ta fuskar raya masana’antu, kasar Sin tana da wani ra’ayi da ya sha bamban da na kasashen yamma, inda kasar Sin ta kan jaddada muhimmancin raya tattalin arziki da inganta bangaren masana’antu a kasashe masu tasowa. Kana yayin da kasar ke neman raya masana’antunta, tana kuma fatan ganin kasashen Afirka sun samu ci gaba na bai daya, da kawo karshen yanayin koma bayan tattalin arziki, da sarrafawa da cin zarafi da kasashen yamma ke yi musu.

Na biyu shi ne, sabanin yadda kasashen yamma ke kallon tsarinsu a matsayin wanda ya fi kyau a duniya, da yadda suke son ba da umarni ga kasashen Afirka, kasar Sin ta kan samar da dabarar raya masana’antu da ta dace da hakikanin yanayin da kasashen Afirka suke ciki.

Labarai Masu Nasaba

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

Misali, ta la’akari da yadda ake fama da karancin tsare-tsaren da za su taimakawa raya masana’antu, da rashin isassun hanyoyin jigilar kayayyaki a Afirka, kasar Sin ta dauki wasu matakai 3 yayin da take aiwatar da ayyukan hadin gwiwa na raya masana’antu a kasashen Afirka: Da farko ta gina dimbin yankunan masana’antu don tabbatar da gudanar ayyukan manyan ma’aikatu yadda ake bukata. Kana na biyu shi ne, kasar Sin da kasashen Afirka sun kirkiro ayyukan masana’antu masu alaka da kayayyakin more rayuwa da aka gina, don tabbatar da cewa kudin da aka kashe wajen gina kayayyakin more rayuwa na samar da amfani da riba. Yayin da na 3 shi ne, kasar Sin na dora muhimmanci kan zuba jari ga masana’antun samar da kayayyakin da ake bukatarsu a kasuwannin kasashen Afirka, lamarin da ya ingiza tsarin raya masana’antu na kasashen Afirka na mai da hankali kan kasuwannin cikin gida, ta yadda ake tabbatar da ci gaban aikin raya bangaren masana’antu a kai a kai.

Ban da haka, dalili na karshe da ya sa nake sa ran ganin amfanin manufar kasar Sin kan raya masana’antu a Afirka shi ne, kasar ta dade tana samar da fasahohin samun ci gaba ga kasashen Afirka, don ciyar da tattalin arzikinsu gaba ta wata ingatacciyar hanya.

Misali, a shekarun baya, karin kasashen dake nahiyar Afirka sun mai da tattalin arziki mai alaka da fasahohin zamani a matsayin sabuwar dabarar neman samun ci gaba, bisa hadin gwiwa da kasar Sin. A kasashen da suka hada da Najeriya da Kenya, da dai sauransu, dandalin biyan kudi ta wayar salula da kamfanoni masu jarin kasar Sin suka kafa na samar da dabarar biyan kudi mai tsaro da sauki ga mutane fiye da miliyan 10. A sa’i daya, kamfanonin kasar Sin sun kaddamar da ayyukan horar da kwararru na fannonin fasahar sadarwa, da ciniki ta yanar gizo ko Internet a kasashen Afirka, inda aka ba dimbin matasan nahiyar Afirka damammaki na koyon fasahohi masu inganci, da wadanda suka shafi kafawa da kula da kamfanoni, ta yadda za a taimakawa kasashen Afirka a fannin zamanantar da fasahohi.

Ta wadannan abubuwa da na bayyana za mu san cewa, kasar Sin na son taimakon kasashen Afirka wajen raya masana’antu, kuma ta san dabara mai dacewa da ya kamata a dauka don taimakawa. Ban da haka, kasar ta dade tana raba fasahohinta masu inganci ga kasashen Afirka, don neman samun ci gaban tattalin arzikinsu na bai daya. Saboda haka, kokarin kasar Sin na raya sabbin fasahohi da sabbin nau’ikan masana’antu tabbas zai samar da damammaki masu kyau na raya tattalin arziki ga kasashen Afirka.

Na kan ji yadda abokaina na Najeriya suke fadin cewa, “A lokacin da kasar Sin ta hau duniyar wata, to, ta tafi tare da Najeriya. ” To, idan kun yarda, zan so in gyara maganar, sa’an nan in sanya ta a karshen wannan sharhi, wato: Lokacin da Sin ta hau duniyar wata, tabbas za a samu kasashen Afirka a can, tare da kasar Sin. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Zamfara Ta Dakatar Da Mambobi 8 Tare Da Rusa Kwamitocinta

Next Post

Gobara Ta Kone Shaguna 50 A Kasuwar ‘Yan Katako A Kano

Related

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

5 days ago
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

6 days ago
Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

1 week ago
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

1 week ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

2 weeks ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

2 weeks ago
Next Post
Hukumar kashe gobara

Gobara Ta Kone Shaguna 50 A Kasuwar 'Yan Katako A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.