• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sace-sace A Zanga-zanga: Ya Kamata Mu Yi Wa Kanmu Fada!

by Sulaiman and Ibrahim Bala
1 year ago
in Ra'ayoyi
0
Sace-sace A Zanga-zanga: Ya Kamata Mu Yi Wa Kanmu Fada!
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.
Da farko kafin na fara cewa komai ina mai jajanta wa al’ummar Nijeriya musamman jahohin Arewa bisa iftila’i na zanga-zanga, domin dole mu kira shi da iftila’i. A ka’ida ta doka babu inda aka hana dan kasa yayi zanga-zangarsa, matsalar da take faruwa wajen yin zanga-zangar wasu batagari sun yi abubuwan da bai kamata ba na sace-sace da dibar kayan mutane.

Kullum Kuka muke na cewar; shuwagabanni ba sa yi mana adalci a wajen shugabancin da suke yi, tunda zabarsu muka yi su yi mana abin da ya dace to, kuma kana kukan cewa kai ka zabi shugaba bai yi maka adalci ba, shugaba baraho ne, kuma kai ka je kana satar kayan wani to, kai da shugaban wane ne barawon?

Wannan kuskure ne, kullum idan har za ka rika biyewa son zuciya muna yarda da irin wannan abun na biyewa son zuciyar mu, haka za mu wayi gari kasar ma ba ta gyaru ba.

Ni a iya tunani na za mu yi wa kanmu fada ne a kan irin wadannan abubuwa da suke faruwa na cewar ina ne sauki, idan Allah bai kawo muku sauki ba babu wanda ya isa ya kawo mana sauki. Na farko mu yi addu’a, domin zagin shugabannin da muke ba fasikanci ba kuskure ne, Allah ya fada duk mutumin daya zalunce ka kana yunkurin neman sakayyarka gurin ubangiji Allah zai saka maka. Na yi imani idan da duk shugaban daya zalunce mu ya zo lokacin zabe muka yi abin da ya dace, wajen zabar ma wanda ya dace muka zaba, da duk ba mu rika fuskantar kanmu a irin wannan kuskuren ba.

A takaice iyaye na gida ‘ya’yanku maza ko mata ku dakatar da su a kan irin abubuwan da suke faruwa, dole ne ka ja kunne a kan danka ya shigo maka da buhun Shinkafa ko katan din Taliya, ko ya zo yana murma wani ya samo galan din mai, idan har ka goyawa danka baya a irin wannan to, a irin haka ne ake fita a harbe danka ba tare da ka’ida ba. Za a yi ta harbe muku ‘ya’ya idan har baku dauki mataki ba, dole ka tsaya ka tsaida gidanka, zanga-zanga ba a hanata ba amma ta lumana ba ta sace-sace da fasa kayan mutane ba.

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Idan kana murna an fasawa wani shago to, ka sani cewar fa kai kuma kana sake murna ne barayi suna kara karuwa a cikinku, dole ne a dakatar. Ina mai bayar da shawara ga kowa idan a kan layi ne kowa a layinsu ya hana dan wani layin ya shigo ya ce zai yi musu wani abu ba daidai ba, a haka–haka idan kowane layi zai dakatar da cewa kowa yayi abinsa a cikin layinsu to, ai ba wanda zai isa yayi sata a layinsu. idan irin wannan za a yi dole ne shuganni su tsaya su kalli mutane su ga me ya kamata ayi?,.

Sannan a gaba ta siyasa ita kuma idan har shugaban kasa sakona ya je gare shi, ina mai bashi shawara da wadannan kudi da ake cewa ana bawa gwamnoni da kayan abinci su rabawa mutane to, dan Allah a canja salo, saboda sako baya zuwa ga talaka domin talakan na kukan cewar; su ba su ma san wannan ana yi ba, a canja salo.

Ko dai a saka musu sauki ta wani bangaren da suke da bukata ko kuma dai a san ya za a yi sakon ya rika zuwa gare su.

A mahanga nan gaba shugaban kasa da wasu shugabannin cewar tainuwa fa biyu suke nema su yi ko tainuwa daya ba a yi ba shekara daya aka yi da wasu watanni, kuma nan gaba kadan za su sake dawowa cikin al’umma neman goyon bayansu su kuma zabarsu a wasu kujerun, to, ni ina mai bayar da shawara shuwagabannin mu ku kalli meye mafita?,

me ya sa ake yin zanga-zangar nan?,

meye za a yi kowa ya koma gida yayi harkokinsa, ana neman sauki a cikin rayuwar?, a’a! tallafin man ne jama’a suke ganin cewar idan ‘Subsidy’ nan ya kamata a sake dawo da shi ko na dan lokaci ne?,

Al’umma su sani, shugabanni su sani kashe su ake yi.

Malamai ku kuma addu’a ya kamata ku yi kune malamai ku ne jagorori addu’a ya kamata ku yi, ba magana ta siyasa ba, su ma kuma ‘yansiyasa kuskure ne ka rika fadar magana a cikin siyasa ka yi abin da za a kawo jahohi da kasa zaman lafiya domin yin maganganun siyasar ma zai iya tada wani tunzurin, ina mai kira da addu’a da mutane, masallatai da kowane lokaci idan aka yi sallah khamsu salawat sallolin nan guda biyar da mu yi addu’a Ubangiji Allah ya kaho mana sauki, duk shugaban da ba alkhairi bane Allah ya gaggauta dauke mana shi ya kaho mana alkhairi, domin Allah ne kadai zai iya fidda mu daga cikin wannan masifa, domin wannan masifa ce. Kada ka ga ba a taba kayanka ba ko ba a kashe naka ba kai ta murna kana jin dadi, Alhaji mu yi addu’a, Malam mu yi addu’a, Hajiya mu yi addu’a, ubangiji Allah ya kaho mana sauki.
Wassalamu Alaikum…


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

Next Post

Jam’iyyar YPP Ta Lashe Kujerar Kansila A Bauchi 

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

5 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

10 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

11 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

11 months ago
BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

11 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

12 months ago
Next Post
Jam’iyyar YPP Ta Lashe Kujerar Kansila A Bauchi 

Jam'iyyar YPP Ta Lashe Kujerar Kansila A Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.