ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sace-sace A Zanga-zanga: Ya Kamata Mu Yi Wa Kanmu Fada!

by Sulaiman and Ibrahim Bala
2 years ago
Zanga-zanga

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.
Da farko kafin na fara cewa komai ina mai jajanta wa al’ummar Nijeriya musamman jahohin Arewa bisa iftila’i na zanga-zanga, domin dole mu kira shi da iftila’i. A ka’ida ta doka babu inda aka hana dan kasa yayi zanga-zangarsa, matsalar da take faruwa wajen yin zanga-zangar wasu batagari sun yi abubuwan da bai kamata ba na sace-sace da dibar kayan mutane.

Kullum Kuka muke na cewar; shuwagabanni ba sa yi mana adalci a wajen shugabancin da suke yi, tunda zabarsu muka yi su yi mana abin da ya dace to, kuma kana kukan cewa kai ka zabi shugaba bai yi maka adalci ba, shugaba baraho ne, kuma kai ka je kana satar kayan wani to, kai da shugaban wane ne barawon?

Wannan kuskure ne, kullum idan har za ka rika biyewa son zuciya muna yarda da irin wannan abun na biyewa son zuciyar mu, haka za mu wayi gari kasar ma ba ta gyaru ba.

ADVERTISEMENT

Ni a iya tunani na za mu yi wa kanmu fada ne a kan irin wadannan abubuwa da suke faruwa na cewar ina ne sauki, idan Allah bai kawo muku sauki ba babu wanda ya isa ya kawo mana sauki. Na farko mu yi addu’a, domin zagin shugabannin da muke ba fasikanci ba kuskure ne, Allah ya fada duk mutumin daya zalunce ka kana yunkurin neman sakayyarka gurin ubangiji Allah zai saka maka. Na yi imani idan da duk shugaban daya zalunce mu ya zo lokacin zabe muka yi abin da ya dace, wajen zabar ma wanda ya dace muka zaba, da duk ba mu rika fuskantar kanmu a irin wannan kuskuren ba.

A takaice iyaye na gida ‘ya’yanku maza ko mata ku dakatar da su a kan irin abubuwan da suke faruwa, dole ne ka ja kunne a kan danka ya shigo maka da buhun Shinkafa ko katan din Taliya, ko ya zo yana murma wani ya samo galan din mai, idan har ka goyawa danka baya a irin wannan to, a irin haka ne ake fita a harbe danka ba tare da ka’ida ba. Za a yi ta harbe muku ‘ya’ya idan har baku dauki mataki ba, dole ka tsaya ka tsaida gidanka, zanga-zanga ba a hanata ba amma ta lumana ba ta sace-sace da fasa kayan mutane ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Idan kana murna an fasawa wani shago to, ka sani cewar fa kai kuma kana sake murna ne barayi suna kara karuwa a cikinku, dole ne a dakatar. Ina mai bayar da shawara ga kowa idan a kan layi ne kowa a layinsu ya hana dan wani layin ya shigo ya ce zai yi musu wani abu ba daidai ba, a haka–haka idan kowane layi zai dakatar da cewa kowa yayi abinsa a cikin layinsu to, ai ba wanda zai isa yayi sata a layinsu. idan irin wannan za a yi dole ne shuganni su tsaya su kalli mutane su ga me ya kamata ayi?,.

Sannan a gaba ta siyasa ita kuma idan har shugaban kasa sakona ya je gare shi, ina mai bashi shawara da wadannan kudi da ake cewa ana bawa gwamnoni da kayan abinci su rabawa mutane to, dan Allah a canja salo, saboda sako baya zuwa ga talaka domin talakan na kukan cewar; su ba su ma san wannan ana yi ba, a canja salo.

Ko dai a saka musu sauki ta wani bangaren da suke da bukata ko kuma dai a san ya za a yi sakon ya rika zuwa gare su.

A mahanga nan gaba shugaban kasa da wasu shugabannin cewar tainuwa fa biyu suke nema su yi ko tainuwa daya ba a yi ba shekara daya aka yi da wasu watanni, kuma nan gaba kadan za su sake dawowa cikin al’umma neman goyon bayansu su kuma zabarsu a wasu kujerun, to, ni ina mai bayar da shawara shuwagabannin mu ku kalli meye mafita?,

me ya sa ake yin zanga-zangar nan?,

meye za a yi kowa ya koma gida yayi harkokinsa, ana neman sauki a cikin rayuwar?, a’a! tallafin man ne jama’a suke ganin cewar idan ‘Subsidy’ nan ya kamata a sake dawo da shi ko na dan lokaci ne?,

Al’umma su sani, shugabanni su sani kashe su ake yi.

Malamai ku kuma addu’a ya kamata ku yi kune malamai ku ne jagorori addu’a ya kamata ku yi, ba magana ta siyasa ba, su ma kuma ‘yansiyasa kuskure ne ka rika fadar magana a cikin siyasa ka yi abin da za a kawo jahohi da kasa zaman lafiya domin yin maganganun siyasar ma zai iya tada wani tunzurin, ina mai kira da addu’a da mutane, masallatai da kowane lokaci idan aka yi sallah khamsu salawat sallolin nan guda biyar da mu yi addu’a Ubangiji Allah ya kaho mana sauki, duk shugaban da ba alkhairi bane Allah ya gaggauta dauke mana shi ya kaho mana alkhairi, domin Allah ne kadai zai iya fidda mu daga cikin wannan masifa, domin wannan masifa ce. Kada ka ga ba a taba kayanka ba ko ba a kashe naka ba kai ta murna kana jin dadi, Alhaji mu yi addu’a, Malam mu yi addu’a, Hajiya mu yi addu’a, ubangiji Allah ya kaho mana sauki.
Wassalamu Alaikum…

Zanga-zanga
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Zanga-zanga
Ibrahim Bala
+ posts Bio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Jam’iyyar YPP Ta Lashe Kujerar Kansila A Bauchi 

Jam'iyyar YPP Ta Lashe Kujerar Kansila A Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.