• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sallah: Yadda Sarkin Gombe Ya Jagoranci Hawan Daba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Sallah: Yadda Sarkin Gombe Ya Jagoranci Hawan Daba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya karbi bakuncin mai martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar da sauran masu sarautar gargajiya a ziyarar bikin babbar sallah.

Hawan dabar na cikin al’adun gargajiya da ake yi duk shekara a gidan gwamnati wanda sarki ke jagorantar hakimai da ‘yan majalisar sarkin.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Kano 
  • Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano

A jawabin da ya gabatar a wajen bikin, Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar, ya yaba tare da jinjina wa gwamnatin jihar bisa kokinta a bangaren kyautata shugabanci da kula da rayuwar al’umma.

Sarkin, wanda shi ne shugaban majalisar sarakunan jihar, ya tabbatar wa Gwamna Inuwa goyon bayan masarautun gargajiya a jihar domin amfanin al’umma baki daya.

Daga bisani sarkin ya jagoranci daruruwan mahaya dawaki a hawan dabar.

Labarai Masu Nasaba

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

A nasa bangaren, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa nasarorin da gwamnatinsa ta samu na da alaka da goyon baya da kyawawan shawarwarin sarakuna da malaman Addini da shugabannin siyasa.

“Nasarorin nan ba ni kadai na same su ba, har da shugabannin siyasa da na gargajiya da na Addini da matasa maza da mata wadanda suka taka rawar gani wajen ganin mun samu wadannan nasarori, don haka muna godiya ga kowa da kowa.”

Kazalika ya bayyana cewa duk da dimbin kalubalen zamantakewa da tattalin arziki da ake fuskanta, gwamnatinsa ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen samar da muhimman ababen more rayuwa ba.

Gwamnan ya yi kira ga sarkin Gombe da sauran sarakunan jihar da kada su yi kasa a gwiwa wajen neman dama da hanyoyin da za su kara kawo ci gaba a jihar.

Ya kuma tabbatarwa jama’ar jihar cewa gwamnatinsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen neman goyon baya daga sarakunan gargajiya domin gudanar da mulkin jihar cikin adalci.

Ya kuma yi godiya ga Allah Madaukakin Sarki da Sarkin Gombe da ya jagoranci ‘yan majalisarsa da sauran al’ummar musulmi zuwa ziyarar a gidan gwamnati domin gudanar da gaisuwar Sallah.

Kazalika Gwamna Inuwa ya mika godiyarsa bisa karramawar da suka yi masa tare da jaddada kokarin gwamnatinsa ga Jihar Gombe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombeHawan DabaInuwa MuhammadSarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Kano 

Next Post

Sin Ta Yi Kira A Mai Da Hankali Kan Hakkin Mata Tsofaffi

Related

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

6 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

7 hours ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

8 hours ago
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

9 hours ago
Neja
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

10 hours ago
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Sin Ta Yi Kira A Mai Da Hankali Kan Hakkin Mata Tsofaffi

Sin Ta Yi Kira A Mai Da Hankali Kan Hakkin Mata Tsofaffi

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.