• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sallah: Yadda Sarkin Gombe Ya Jagoranci Hawan Daba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya karbi bakuncin mai martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar da sauran masu sarautar gargajiya a ziyarar bikin babbar sallah.

Hawan dabar na cikin al’adun gargajiya da ake yi duk shekara a gidan gwamnati wanda sarki ke jagorantar hakimai da ‘yan majalisar sarkin.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Kano 
  • Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano

A jawabin da ya gabatar a wajen bikin, Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar, ya yaba tare da jinjina wa gwamnatin jihar bisa kokinta a bangaren kyautata shugabanci da kula da rayuwar al’umma.

Sarkin, wanda shi ne shugaban majalisar sarakunan jihar, ya tabbatar wa Gwamna Inuwa goyon bayan masarautun gargajiya a jihar domin amfanin al’umma baki daya.

Daga bisani sarkin ya jagoranci daruruwan mahaya dawaki a hawan dabar.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

A nasa bangaren, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa nasarorin da gwamnatinsa ta samu na da alaka da goyon baya da kyawawan shawarwarin sarakuna da malaman Addini da shugabannin siyasa.

“Nasarorin nan ba ni kadai na same su ba, har da shugabannin siyasa da na gargajiya da na Addini da matasa maza da mata wadanda suka taka rawar gani wajen ganin mun samu wadannan nasarori, don haka muna godiya ga kowa da kowa.”

Kazalika ya bayyana cewa duk da dimbin kalubalen zamantakewa da tattalin arziki da ake fuskanta, gwamnatinsa ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen samar da muhimman ababen more rayuwa ba.

Gwamnan ya yi kira ga sarkin Gombe da sauran sarakunan jihar da kada su yi kasa a gwiwa wajen neman dama da hanyoyin da za su kara kawo ci gaba a jihar.

Ya kuma tabbatarwa jama’ar jihar cewa gwamnatinsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen neman goyon baya daga sarakunan gargajiya domin gudanar da mulkin jihar cikin adalci.

Ya kuma yi godiya ga Allah Madaukakin Sarki da Sarkin Gombe da ya jagoranci ‘yan majalisarsa da sauran al’ummar musulmi zuwa ziyarar a gidan gwamnati domin gudanar da gaisuwar Sallah.

Kazalika Gwamna Inuwa ya mika godiyarsa bisa karramawar da suka yi masa tare da jaddada kokarin gwamnatinsa ga Jihar Gombe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Sin Ta Yi Kira A Mai Da Hankali Kan Hakkin Mata Tsofaffi

Sin Ta Yi Kira A Mai Da Hankali Kan Hakkin Mata Tsofaffi

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.