ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sallah: Yadda Sarkin Gombe Ya Jagoranci Hawan Daba

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gombe

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya karbi bakuncin mai martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar da sauran masu sarautar gargajiya a ziyarar bikin babbar sallah.

Hawan dabar na cikin al’adun gargajiya da ake yi duk shekara a gidan gwamnati wanda sarki ke jagorantar hakimai da ‘yan majalisar sarkin.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Kano 
  • Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano

A jawabin da ya gabatar a wajen bikin, Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar, ya yaba tare da jinjina wa gwamnatin jihar bisa kokinta a bangaren kyautata shugabanci da kula da rayuwar al’umma.

ADVERTISEMENT

Sarkin, wanda shi ne shugaban majalisar sarakunan jihar, ya tabbatar wa Gwamna Inuwa goyon bayan masarautun gargajiya a jihar domin amfanin al’umma baki daya.

Daga bisani sarkin ya jagoranci daruruwan mahaya dawaki a hawan dabar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

A nasa bangaren, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa nasarorin da gwamnatinsa ta samu na da alaka da goyon baya da kyawawan shawarwarin sarakuna da malaman Addini da shugabannin siyasa.

“Nasarorin nan ba ni kadai na same su ba, har da shugabannin siyasa da na gargajiya da na Addini da matasa maza da mata wadanda suka taka rawar gani wajen ganin mun samu wadannan nasarori, don haka muna godiya ga kowa da kowa.”

Kazalika ya bayyana cewa duk da dimbin kalubalen zamantakewa da tattalin arziki da ake fuskanta, gwamnatinsa ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen samar da muhimman ababen more rayuwa ba.

Gwamnan ya yi kira ga sarkin Gombe da sauran sarakunan jihar da kada su yi kasa a gwiwa wajen neman dama da hanyoyin da za su kara kawo ci gaba a jihar.

Ya kuma tabbatarwa jama’ar jihar cewa gwamnatinsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen neman goyon baya daga sarakunan gargajiya domin gudanar da mulkin jihar cikin adalci.

Ya kuma yi godiya ga Allah Madaukakin Sarki da Sarkin Gombe da ya jagoranci ‘yan majalisarsa da sauran al’ummar musulmi zuwa ziyarar a gidan gwamnati domin gudanar da gaisuwar Sallah.

Kazalika Gwamna Inuwa ya mika godiyarsa bisa karramawar da suka yi masa tare da jaddada kokarin gwamnatinsa ga Jihar Gombe.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Kira A Mai Da Hankali Kan Hakkin Mata Tsofaffi

Sin Ta Yi Kira A Mai Da Hankali Kan Hakkin Mata Tsofaffi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.