ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sallah: Yadda Sarkin Gombe Ya Jagoranci Hawan Daba

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gombe

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya karbi bakuncin mai martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar da sauran masu sarautar gargajiya a ziyarar bikin babbar sallah.

Hawan dabar na cikin al’adun gargajiya da ake yi duk shekara a gidan gwamnati wanda sarki ke jagorantar hakimai da ‘yan majalisar sarkin.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Kano 
  • Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano

A jawabin da ya gabatar a wajen bikin, Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar, ya yaba tare da jinjina wa gwamnatin jihar bisa kokinta a bangaren kyautata shugabanci da kula da rayuwar al’umma.

ADVERTISEMENT

Sarkin, wanda shi ne shugaban majalisar sarakunan jihar, ya tabbatar wa Gwamna Inuwa goyon bayan masarautun gargajiya a jihar domin amfanin al’umma baki daya.

Daga bisani sarkin ya jagoranci daruruwan mahaya dawaki a hawan dabar.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

A nasa bangaren, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa nasarorin da gwamnatinsa ta samu na da alaka da goyon baya da kyawawan shawarwarin sarakuna da malaman Addini da shugabannin siyasa.

“Nasarorin nan ba ni kadai na same su ba, har da shugabannin siyasa da na gargajiya da na Addini da matasa maza da mata wadanda suka taka rawar gani wajen ganin mun samu wadannan nasarori, don haka muna godiya ga kowa da kowa.”

Kazalika ya bayyana cewa duk da dimbin kalubalen zamantakewa da tattalin arziki da ake fuskanta, gwamnatinsa ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen samar da muhimman ababen more rayuwa ba.

Gwamnan ya yi kira ga sarkin Gombe da sauran sarakunan jihar da kada su yi kasa a gwiwa wajen neman dama da hanyoyin da za su kara kawo ci gaba a jihar.

Ya kuma tabbatarwa jama’ar jihar cewa gwamnatinsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen neman goyon baya daga sarakunan gargajiya domin gudanar da mulkin jihar cikin adalci.

Ya kuma yi godiya ga Allah Madaukakin Sarki da Sarkin Gombe da ya jagoranci ‘yan majalisarsa da sauran al’ummar musulmi zuwa ziyarar a gidan gwamnati domin gudanar da gaisuwar Sallah.

Kazalika Gwamna Inuwa ya mika godiyarsa bisa karramawar da suka yi masa tare da jaddada kokarin gwamnatinsa ga Jihar Gombe.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Kira A Mai Da Hankali Kan Hakkin Mata Tsofaffi

Sin Ta Yi Kira A Mai Da Hankali Kan Hakkin Mata Tsofaffi

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.