• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sama Da Mutum 100 Sun Mutu A Ambaliyar Ruwa A Ruwanda

bySadiq
2 years ago
Ambaliyar Ruwa

Akalla mutane 109 ne suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a arewaci da yammacin kasar Rwanda, in ji hukumar yada labaran kasar RBA a jiya Laraba, inda ta ambato alkalumma daga hukumomin kasar.

“Ruwan da aka yi a daren jiya ya haifar da iftila’i a lardunan Arewa da na Yamma,” in ji RBA a shafinta na yanar gizo.

  • Sakon Buhari Ga ‘Yan Jarida: Na Kare ‘Yancinku
  • ‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Kungiyar Asiri 55 A Ribas

“A halin yanzu, alkalumman wucin gadi da hukumomin wadannan lardunan suka wallafa sun ce an sanar da mutuwar mutane 109.”

Mai watsa labaran ya ce har yanzu ruwan na karuwa, wanda ke haifar da barazana ga karin rayuka.

Hukumar ta ce mutane 95 ne suka mutu a Lardin Yamma da ya fi fama da iftila’in da kuma wasu 14 a Lardin Arewa, inda aka ce ambaliyar ruwan ta yi awon gaba da gidaje da ababen more rayuwa tare da rufe hanyoyi.

LABARAI MASU NASABA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

Hotunan da aka yada a shafin RBA na Twitter sun nuna cewa gidaje sun lalace, hanyoyin da zaftarewar kasa suka yanke da kuma filayen da ruwan ya mamaye.

“An fara kokarin ba da agaji nan da nan, ciki har da taimaka wa wajen binne wadanda iftila’in ya shafa da kuma samar da kayayyaki ga wadanda gidajensu ya lalace,” in ji ministar da ke kula da ayyukan gaggawa, Marie Solange Kayisire.

Ta yi kira ga mazauna yankin da su kwashe mutane zuwa wuri mafi inganci idan ana ruwan sama kamar da bakin kwarya.

A makwabciyar kasar Uganda, mutane shida ne suka mutu a yammacin kasar, sakamakon zaftarewar kasa da afkawar gidajensu, bayan da aka shafe kwanaki ana ruwan sama kamar da bakin kwarya, a cewar kungiyar agaji ta Red Cross.

An ce biyar daga cikin wadanda suka mutu ‘yan gida daya ne kuma ‘yan kauye daya ne.

A watan Mayun shekarar 2020, akalla mutane 65 ne suka mutu a kasar Ruwanda sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a gabashin Afirka, yayin da aka samu rahoton mutuwar akalla mutane 194 a Kenya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Sin: An Gudanar Da Tafiye Tafiye Sama Da Miliyan 274 Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Na Bana

Sin: An Gudanar Da Tafiye Tafiye Sama Da Miliyan 274 Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version