ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sama Da Mutum 100 Sun Mutu A Ambaliyar Ruwa A Ruwanda

by Sadiq
3 years ago
Ambaliyar Ruwa

Akalla mutane 109 ne suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a arewaci da yammacin kasar Rwanda, in ji hukumar yada labaran kasar RBA a jiya Laraba, inda ta ambato alkalumma daga hukumomin kasar.

“Ruwan da aka yi a daren jiya ya haifar da iftila’i a lardunan Arewa da na Yamma,” in ji RBA a shafinta na yanar gizo.

  • Sakon Buhari Ga ‘Yan Jarida: Na Kare ‘Yancinku
  • ‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Kungiyar Asiri 55 A Ribas

“A halin yanzu, alkalumman wucin gadi da hukumomin wadannan lardunan suka wallafa sun ce an sanar da mutuwar mutane 109.”

ADVERTISEMENT

Mai watsa labaran ya ce har yanzu ruwan na karuwa, wanda ke haifar da barazana ga karin rayuka.

Hukumar ta ce mutane 95 ne suka mutu a Lardin Yamma da ya fi fama da iftila’in da kuma wasu 14 a Lardin Arewa, inda aka ce ambaliyar ruwan ta yi awon gaba da gidaje da ababen more rayuwa tare da rufe hanyoyi.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Hotunan da aka yada a shafin RBA na Twitter sun nuna cewa gidaje sun lalace, hanyoyin da zaftarewar kasa suka yanke da kuma filayen da ruwan ya mamaye.

“An fara kokarin ba da agaji nan da nan, ciki har da taimaka wa wajen binne wadanda iftila’in ya shafa da kuma samar da kayayyaki ga wadanda gidajensu ya lalace,” in ji ministar da ke kula da ayyukan gaggawa, Marie Solange Kayisire.

Ta yi kira ga mazauna yankin da su kwashe mutane zuwa wuri mafi inganci idan ana ruwan sama kamar da bakin kwarya.

A makwabciyar kasar Uganda, mutane shida ne suka mutu a yammacin kasar, sakamakon zaftarewar kasa da afkawar gidajensu, bayan da aka shafe kwanaki ana ruwan sama kamar da bakin kwarya, a cewar kungiyar agaji ta Red Cross.

An ce biyar daga cikin wadanda suka mutu ‘yan gida daya ne kuma ‘yan kauye daya ne.

A watan Mayun shekarar 2020, akalla mutane 65 ne suka mutu a kasar Ruwanda sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a gabashin Afirka, yayin da aka samu rahoton mutuwar akalla mutane 194 a Kenya.

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
Sin: An Gudanar Da Tafiye Tafiye Sama Da Miliyan 274 Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Na Bana

Sin: An Gudanar Da Tafiye Tafiye Sama Da Miliyan 274 Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.