ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sama Da Mutum 100 Sun Mutu A Ambaliyar Ruwa A Ruwanda

by Sadiq
3 years ago
Ambaliyar Ruwa

Akalla mutane 109 ne suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a arewaci da yammacin kasar Rwanda, in ji hukumar yada labaran kasar RBA a jiya Laraba, inda ta ambato alkalumma daga hukumomin kasar.

“Ruwan da aka yi a daren jiya ya haifar da iftila’i a lardunan Arewa da na Yamma,” in ji RBA a shafinta na yanar gizo.

  • Sakon Buhari Ga ‘Yan Jarida: Na Kare ‘Yancinku
  • ‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Kungiyar Asiri 55 A Ribas

“A halin yanzu, alkalumman wucin gadi da hukumomin wadannan lardunan suka wallafa sun ce an sanar da mutuwar mutane 109.”

ADVERTISEMENT

Mai watsa labaran ya ce har yanzu ruwan na karuwa, wanda ke haifar da barazana ga karin rayuka.

Hukumar ta ce mutane 95 ne suka mutu a Lardin Yamma da ya fi fama da iftila’in da kuma wasu 14 a Lardin Arewa, inda aka ce ambaliyar ruwan ta yi awon gaba da gidaje da ababen more rayuwa tare da rufe hanyoyi.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Hotunan da aka yada a shafin RBA na Twitter sun nuna cewa gidaje sun lalace, hanyoyin da zaftarewar kasa suka yanke da kuma filayen da ruwan ya mamaye.

“An fara kokarin ba da agaji nan da nan, ciki har da taimaka wa wajen binne wadanda iftila’in ya shafa da kuma samar da kayayyaki ga wadanda gidajensu ya lalace,” in ji ministar da ke kula da ayyukan gaggawa, Marie Solange Kayisire.

Ta yi kira ga mazauna yankin da su kwashe mutane zuwa wuri mafi inganci idan ana ruwan sama kamar da bakin kwarya.

A makwabciyar kasar Uganda, mutane shida ne suka mutu a yammacin kasar, sakamakon zaftarewar kasa da afkawar gidajensu, bayan da aka shafe kwanaki ana ruwan sama kamar da bakin kwarya, a cewar kungiyar agaji ta Red Cross.

An ce biyar daga cikin wadanda suka mutu ‘yan gida daya ne kuma ‘yan kauye daya ne.

A watan Mayun shekarar 2020, akalla mutane 65 ne suka mutu a kasar Ruwanda sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a gabashin Afirka, yayin da aka samu rahoton mutuwar akalla mutane 194 a Kenya.

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Next Post
Sin: An Gudanar Da Tafiye Tafiye Sama Da Miliyan 274 Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Na Bana

Sin: An Gudanar Da Tafiye Tafiye Sama Da Miliyan 274 Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.